Skip to main content

ZAN YI AZUMI TALATIN DA DAYA (31)

Tambaya


Assalamu Alaikum malam Tambayata ita ce malam idan mutum ya fara Azimi a qasar Nigeria, sai yaje wata qasa misali qasar saudiya sai Azuminsu ya kai talatin, kai kuma idan ka ida wannan Azumi tare da su to Azuminka zai zama talatin da daya, menene mafita ?


Amsa

Waa alaikumus Salam, 
To dan'uwa za ka cigaba da azumi ne tare da su, har sai sun sauke, saboda fadin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi : "Ana shan ruwa ne ranar da mutane suka sha ruwa" kamar yadda Tirmizi ya rawaito a hadisi mai lamba ta : 697 kuma Albani ya inganta shi a silsilatussahihah 224 .
A bisa wannan hadisin wanda ya je Saudiyya a wannan shekarar ta 1435, ba zai sauke azumi ba har sai sun sauke, ko da kuwa zai yi talatin da daya ne, kamar yadda wanda ya dauko daga Saudiyya ya taho Nigeria zai sauke azuminsa lokacin da suka sauke, ko da kuwa zai zama ashirin da takwas ne, saidai zai rama daya bayan sallah.

Allah ne mafi sani 

Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

Comments

Popular posts from this blog

Addu'ar Neman Mijin/Matar Aure

TAMBAYA Assalamu Alaikum warahmatullah malam don Allah ina Neman fatawane Watace take Neman miji kasancewar duk masu  zuwa wurinta ba dagaske suke yi ba toh shi ne ta nemi taimako wurin malamin zaure yake bata rubutu tana sha daniyyar Allah ya sa ta dace. Toh malam abin tambaya anan shi ne shin menene makomar abin da ta aikata? shin malam tayi shirka ne ko kuwa tayi ba daidai ba? nagode. AMSA    Dafarko gameda shan rubutu muddin ayan QUR'ANI ne tsantsa babu wasu zane zanen hatimi, to ya halatta yadda IBN TAIMIYYA ya tabbatar a MAJMU'UL FATAWA, haka ma WAHEED ABDUSSALAM BAALY ya tabbar da hakan a SARIMUL BATTAR,    Amma in akasin haka ne haramun ne don yakan zama shirka ne da surkulle,    Fadin cewa Malamin zaure ne na gargajiya to galibi irin na shirkan sukeyi, don haka ki tuba tsakanin ki da ALLAH da alkawarin bazaki sake zuwa wurin su ba don kare addinin ki da mutuncin ki,    Don samun biyan bukatun ki sai kizage da addu'a da kiyamul...

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI Fitowa na 3

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI               NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 3 (kuma fitowa ta karshe): HAKKOKIN MACE A KAN MIJINTA: Kamar yadda miji yake da hakkoki akan matarsa, haka ita ma matar take da hakkokin akan mijinta, daga cikin wadannan hakkoki akwai : 1 - SADAKI: Hakkin mace ne a bata sadakinta, yayin da za a aure ta, Allah Madaukakin Sarki ya ce: “Ku bawa mata sadakinsu kyauta” (Nisa’i 4). A wani wurin Allah Madaukakin Sarki cewa ya yi:   “Ku aure su da izinin iyalansu, ku basu sadakinsu da adalci” (Addalak : 25). 2 – CIYARWA: Hakkin mata ne akan mijinta ya ciyar da ita, gwargwadon halinsa, koda kuwa tana da wadata da arziki, Allah Madaukakin Sarki yana cewa :  “Mai wadata ya ciyar daga wadatarsa, wanda kuwa aka kuntatawa arzikinsa, to ya ciyar daga abin da Allah ya bashi, Allah baya dorawa wata rai sai abin da ya bata” (Dalaq : 7). An tambayi Manzon Allah, tsira da amincin ...

HUKUNCIN HADA SITTU SHAWWAL DA RAMUWAR RAMADAN

Tambaya : Assalamu alaikum Malam idan ana binka ramuwar azimi za ka iya niyya biyu : wato da nufin sittu shawwal da ramuwar Ramadhana a guda daya ? don Allah mlm taimaka min da bayani. Amsa :  Wa alaikum assalamu To 'yar'uwa kowanne daban ake yinsa, saboda manufarsu ta banbanta, don haka ba za'a hada su da niyya daya ba, kamar yadda ake yi a wankan janaba da wankan juma'a, za mu fahimci haka, a cikin fadin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi : "Duk wanda ya azumci Ramadhana sannan ya biyar da kwanaki shida na Shawwal, Allah zai ba shi ladan wanda ya yi azumin shekara" Muslim ya rawaito shi a hadisi mai lamba ta : 1164, kin ga wannan yana nuna Ramadan daban, sittu-shawwal daban. Fadin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi : " Sannan ya biyar da kwanaki shida na Shawwal" ya sa wasu malaman sun tafi akan cewa : bai halatta ayi sittu-shawwal ba, sai bayan an kammala ramuwar Ramadan. Kamar yadda ya zo a : sharhurmumti...