Skip to main content

Huduba Daga Masallaci Mai Alfarma Yau Jum'ah 18 ga Dhul Hajj 1436H (2/10/2015)

Huduba Daga Masallaci Mai Alfarma
Yau Jum'ah 18 ga Dhul Hajj 1436H (2/10/2015)

A yau Sheikh Su'ud As-Shuraim - daya daga cikin limaman masallaci mai alfarma - ne ya jagoranci sallah a masallacin Makka mai daraja bayan ya yi huduba a kan cikar addini da hadarin yin bidi'a a cikin sa.
Sheikh ya soma hudubarsa da gode ma Allah a kan ni'imar kammala aikin Hajji wanda a tsakiyar aiwatar da shi ne Allah ya shelanta ma manzonsa cewa ya cika ma wannan al'umma addininta.
A cikin wannan Hajji Manzon Allah (S) ya yi hasashen kusantowar ajalinsa.
Limamin ya fashe da kuka a lokacin da yake bayanin kamalar addinin musulunci da kasancewar manzon Allah (S) bai bar wani abu da ake bukatar bayanin sa a addini ba face ya bayyana shi kafin zuwan ajalinsa. Amma kuma musulmi da yawa ba su fahimci haka ba. Sai aka hada gaskiya da karya, aka farar da sababbin abubuwa da sunan wai musulunci dole ne ya  canza riga don ya dace da zamani. Akwai mamaki ace kafiri arne wanda ya rayu a cikin musulmi ya fi musulmin fahimtar wannan aya. Domin wani bayahude ya ce ma Sayyidi Umar akwai aya a cikin littafinku in da muna da irin ta da mun mayar da ranar saukar ta ranar buki ta shekara shekara. Yana nuni zuwa ga sanin muhimmancin kammala addini, abinda musulmi da yawa ba su fahimce shi ba.
A yau wasu wawaye sun mayar da addini bakauye, suna dauka cewa, ba zai dace da zamani ba wai sai an yi masa gyaran fuska.
Ku sani ya ku musulmi! Wallahi babu sadda zamu iya shiga gaban manzon Allah ko mu fi shi iya ganewa da fahimtar addini.
Allah ya cika addininmu, bai bar wani alheri ba sai da ya nuna mana shi. Kuma duk wata lalura da zata faru ko wata bukata da za ta auku ga yan Adam akwai bayanin ta a cikin musulunci ba sai mun yi aro daga wajen sa ba.
Musulunci ya karantar da yan uwantaka da kyautatawa da fahimtar juna, duk a karkashin Kalimatus Shahada.
Allah ya yi kira ga mu  kauce ma shaidan wanda babban makiyi ne a gare mu.
A cikin huduba ta biyu, liman ya jaddada gode ma Allah sannan ya ce, duk matsalolin da al'umma take fama da su ba sababbi ba ne kuma ba wani abu ya jawo su ba sai kauce ma hanya da musulmi suke yi. Abinda yake faruwa a Syria zalunci ne da ake yi a kan talakawa.
Sannan liman ya yi nuni ga hassada da kyashin da kasar Iran take yi ma kasa mai tsarki da kulle kullen da take yi mata dare da rana yana mai nuni ga abinda suka haifar na tashin hankula da kashe jama'a sannan suka ruga majalisar dunkin duniya suna cewa Saudi ba ta iya ba. A ba su dama su shigo kasa mai tsarki su yi hidimar alhazai. Ya ce, a wannan kasa muna da doka, muna da tsari, a kan Sharia muke tafiya, kuma ba zamu taba buda kofa a wargaza mana akida ko a taba mana zaman lafiya ba. Kuma maganar Allah ba ta tashi, lalle ne zai taimaki muminai.
Liman ya rufe hudubarsa da addu'oi masu kyau masu dadi, masu albarka.
Ya sake fashewa da kuka a lokacin da yake yi ma alhazzai addu'a musamman wadanda suka hadu da matsaloli da jarabawa a cikin aikin hajji.
Ya Allah ka karbi adduoinsa, ka wanzar da aminci a cikin musulmi, ka kare mu daga makircin makiya.
Fassara daga Dr Mansur Sokoto.

Comments

  1. https://fiqhussunnah.blogspot.com/2015/11/huduba-daga-masallaci-mai-alfarma-yau.html?showComment=1538185184096#c5120439243557533275

    ReplyDelete
  2. This comment has been removed by a blog administrator.

    ReplyDelete

Post a Comment

Popular posts from this blog

Addu'ar Neman Mijin/Matar Aure

TAMBAYA Assalamu Alaikum warahmatullah malam don Allah ina Neman fatawane Watace take Neman miji kasancewar duk masu  zuwa wurinta ba dagaske suke yi ba toh shi ne ta nemi taimako wurin malamin zaure yake bata rubutu tana sha daniyyar Allah ya sa ta dace. Toh malam abin tambaya anan shi ne shin menene makomar abin da ta aikata? shin malam tayi shirka ne ko kuwa tayi ba daidai ba? nagode. AMSA    Dafarko gameda shan rubutu muddin ayan QUR'ANI ne tsantsa babu wasu zane zanen hatimi, to ya halatta yadda IBN TAIMIYYA ya tabbatar a MAJMU'UL FATAWA, haka ma WAHEED ABDUSSALAM BAALY ya tabbar da hakan a SARIMUL BATTAR,    Amma in akasin haka ne haramun ne don yakan zama shirka ne da surkulle,    Fadin cewa Malamin zaure ne na gargajiya to galibi irin na shirkan sukeyi, don haka ki tuba tsakanin ki da ALLAH da alkawarin bazaki sake zuwa wurin su ba don kare addinin ki da mutuncin ki,    Don samun biyan bukatun ki sai kizage da addu'a da kiyamul...

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI Fitowa na 3

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI               NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 3 (kuma fitowa ta karshe): HAKKOKIN MACE A KAN MIJINTA: Kamar yadda miji yake da hakkoki akan matarsa, haka ita ma matar take da hakkokin akan mijinta, daga cikin wadannan hakkoki akwai : 1 - SADAKI: Hakkin mace ne a bata sadakinta, yayin da za a aure ta, Allah Madaukakin Sarki ya ce: “Ku bawa mata sadakinsu kyauta” (Nisa’i 4). A wani wurin Allah Madaukakin Sarki cewa ya yi:   “Ku aure su da izinin iyalansu, ku basu sadakinsu da adalci” (Addalak : 25). 2 – CIYARWA: Hakkin mata ne akan mijinta ya ciyar da ita, gwargwadon halinsa, koda kuwa tana da wadata da arziki, Allah Madaukakin Sarki yana cewa :  “Mai wadata ya ciyar daga wadatarsa, wanda kuwa aka kuntatawa arzikinsa, to ya ciyar daga abin da Allah ya bashi, Allah baya dorawa wata rai sai abin da ya bata” (Dalaq : 7). An tambayi Manzon Allah, tsira da amincin ...

Hakkokin Ma'aurata a Shari'ar Musulunci Fitowa na 2

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI       NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 2 3 -  YIN ADO DA KWALLIYA: Hakkin miji ne akan matarsa ta yi masa ado da kwalliya, don ta kare shi daga kallon wasu matan daban, wadanda shari’a ta hana shi kallonsu. Mata sun kasance suna kwalliya da dan kunne da awarwaro da munduwa tun a zamanin Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kamar yadda hadisin Abdullahi dan Abbas, Allah Ya kara yarda a gare shi a cikin Sahihul Bukhari da Muslim ya nuna, a lokacin da Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya je wajensu, ya yi musu wa’azi a ranar idi. Kuma saboda Mahimmanci mace ta yi wa mijinta kwalliya, ta zama a shiga mai kyau mai jan hankali, Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya hana miji ya dawo wa iyalinsa daga tafiya cikin dare, ya shigo gida ba tare da sun san da zuwansa ba, An karbo daga Jabir, Allah Ya kara yarda a gare shi, ya ce, Manz...