Skip to main content

MUT'A KO DAI ZINA! Fitowa ta 2

MUT'A KO DAI ZINA!

             NA
Muhammad Umar Ibrahim Gumau

FITOWA TA 2:

MA'ANAR MUT'A  A SHI'A.

Wakikci yana halatta a cikin wannan kulli daga dukkan ma'auratan biyu, kamar waninsa na kulle-kulle. Kuma da cikarsa be take zama mata a gare ka, kai kuma ka kake zama miji a gare ta, har zuwa karshen ajalin da aka ambata a cikin kulli (auren). Kuma yana karewa zata nisance ka ba tare da saki ba kamar jinga. Kuma mijin ya samu ya rabu da ita gabanin karewar ajalin da kyatar sauran kwanakin da suka rage ba tare da saki ba. Kuma yana wajaba tayi idda bayan ya take ta bayan kyautar lokacin ko karewarsa da tsarki biyu idan ta kasance daga cikin mata masu haila. Idan kuwa ba ta kasance daga cikin mata masu haila ba said ta yi idda ta kwana arba'in da biyar kamar baiwa".

ABUBUWAN DA MAI KARATU ZAI FAHIMTA:-

Lallai a cikin wannan ma'ana ta auren mut'a da shi wannan malamin shi'a ya ba mu, mai karatu zai fahimci abubuwa kamar haka:-

(a) Auren babu waliyyi, daga ita said shi aukayi,
(b) Itace ta aurar da kanta
(c)  Abdul Husain bai ambaci daya daga cikin sharuddan aure ba kamar haka:- waliyyi, sadaki, shedu, ciyarwa, wurin kwana, saki, gado, da dai sauransu, sai dai ya ambaci dukiyar da zai bata (kamar dai yadda ake ba karuwa kudin jinga).
(d) Samuwar sharadi a cikin sa, na zuwa wani lokaci ayyananne wanda auren na karewa da karewar sa saboda haka shi wannan aure bashi da wani sharadi ingancin aure na sharia.

MAKIRCIN SHI'A A CIKIN  WANNAN MA'ANAR

Muhadu a fitowa ta uku insha Allahu



Ga dukkan mai son shiga ZAUREN FIQHUS SUNNAH, sai ya yi saving wannan number 08142082937 sannan ya aika da cikakken sunansa da adireshinsa.

Comments

Popular posts from this blog

Addu'ar Neman Mijin/Matar Aure

TAMBAYA Assalamu Alaikum warahmatullah malam don Allah ina Neman fatawane Watace take Neman miji kasancewar duk masu  zuwa wurinta ba dagaske suke yi ba toh shi ne ta nemi taimako wurin malamin zaure yake bata rubutu tana sha daniyyar Allah ya sa ta dace. Toh malam abin tambaya anan shi ne shin menene makomar abin da ta aikata? shin malam tayi shirka ne ko kuwa tayi ba daidai ba? nagode. AMSA    Dafarko gameda shan rubutu muddin ayan QUR'ANI ne tsantsa babu wasu zane zanen hatimi, to ya halatta yadda IBN TAIMIYYA ya tabbatar a MAJMU'UL FATAWA, haka ma WAHEED ABDUSSALAM BAALY ya tabbar da hakan a SARIMUL BATTAR,    Amma in akasin haka ne haramun ne don yakan zama shirka ne da surkulle,    Fadin cewa Malamin zaure ne na gargajiya to galibi irin na shirkan sukeyi, don haka ki tuba tsakanin ki da ALLAH da alkawarin bazaki sake zuwa wurin su ba don kare addinin ki da mutuncin ki,    Don samun biyan bukatun ki sai kizage da addu'a da kiyamul...

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI Fitowa na 3

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI               NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 3 (kuma fitowa ta karshe): HAKKOKIN MACE A KAN MIJINTA: Kamar yadda miji yake da hakkoki akan matarsa, haka ita ma matar take da hakkokin akan mijinta, daga cikin wadannan hakkoki akwai : 1 - SADAKI: Hakkin mace ne a bata sadakinta, yayin da za a aure ta, Allah Madaukakin Sarki ya ce: “Ku bawa mata sadakinsu kyauta” (Nisa’i 4). A wani wurin Allah Madaukakin Sarki cewa ya yi:   “Ku aure su da izinin iyalansu, ku basu sadakinsu da adalci” (Addalak : 25). 2 – CIYARWA: Hakkin mata ne akan mijinta ya ciyar da ita, gwargwadon halinsa, koda kuwa tana da wadata da arziki, Allah Madaukakin Sarki yana cewa :  “Mai wadata ya ciyar daga wadatarsa, wanda kuwa aka kuntatawa arzikinsa, to ya ciyar daga abin da Allah ya bashi, Allah baya dorawa wata rai sai abin da ya bata” (Dalaq : 7). An tambayi Manzon Allah, tsira da amincin ...

Hakkokin Ma'aurata a Shari'ar Musulunci Fitowa na 2

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI       NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 2 3 -  YIN ADO DA KWALLIYA: Hakkin miji ne akan matarsa ta yi masa ado da kwalliya, don ta kare shi daga kallon wasu matan daban, wadanda shari’a ta hana shi kallonsu. Mata sun kasance suna kwalliya da dan kunne da awarwaro da munduwa tun a zamanin Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kamar yadda hadisin Abdullahi dan Abbas, Allah Ya kara yarda a gare shi a cikin Sahihul Bukhari da Muslim ya nuna, a lokacin da Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya je wajensu, ya yi musu wa’azi a ranar idi. Kuma saboda Mahimmanci mace ta yi wa mijinta kwalliya, ta zama a shiga mai kyau mai jan hankali, Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya hana miji ya dawo wa iyalinsa daga tafiya cikin dare, ya shigo gida ba tare da sun san da zuwansa ba, An karbo daga Jabir, Allah Ya kara yarda a gare shi, ya ce, Manz...