Skip to main content

MUT'A KO DAI ZINA! Fitowa ta 3

MUT'A KO DAI ZINA!

             NA
Muhammad Umar Ibrahim Gumau

FITOWA TA 3:

MAKIRCIN SHI'A A CIKIN WANNAN MA'ANAR

Karyar Abdul Husain, inda yake cewa: wanda babu abin da shari'a ta hana Alhali babu sharuddan aure a cikin sa.

      FADAKARWA

Wannan ma'ana ta sabawa abinda na karanta a cikin Alkafi, daga "Abbana Dan Tagliba" yace: na cewa Abu Abdullahi (AS): Yaya zance mata idan na kadaita da ita? Sai yace: za ka ce ne: " Na aure ki auren mut'a a bisa littafin Allah da sunnar AnnabinSa (SAW) ba za ki yi gado ba kuma ba za a gaje ki ba tsawon kwana kaza-da-kaza. Idan kuma ka so, shekara kaza-da-kaza, da kaza-da-kaza na dirham. Sai ka ambaci abinda duk kuka yi yardatayya a kansa na lada, kadan ne ko mai yawa. Idan tace "na'am" to hakika ta yarda, saboda haka ta zamo matarka kai kuma ka zamo mijinta kuma mafi cancantar mutane da ita.

MUT'A A WURIN 'YAN SHI'A

Lallai mut'a tana da mahimmanci kwarai a wurin 'yan shi'a saboda haka suka kirkiro mata munanan Hadisai na karya, suna jinginasu zuwa ga Imaman Ahlul Baiti (AS), alhalin Imaman Ahlul Baiti sun barranta daga gare su irin barrantar kekeci daga jinin dan Annabi Ya'kub (AS). Saboda kada in tsawaita zan takaita da Hadisi daya kawai. Suna cewa wai Manzon Allah (SAW) yace: Duk wanda yayi mut'a sau daya darajarsa ta kasance kamar darajar Alhusain (AS) Imam na uku a wurin 'yan Shi'a, kuma duk wanda yayi mut'a sau biyu darajarsa ta kasance kamar darajar Alhasan (AS), Imam na biyu a wurinsu, kuma duk wanda yayi mut'a sau uku darajarsa ta kasance kamar darajar Aliyu Dan Abi Talib (RA) Imam na farko a wurinsu, kuma duk wanda yayi mut'a sau hudu darajarsa kamar darajata".

Nake cewa: ya kai mai karatu kaji duk wanda yayi mut'a sau hudu ya riski Annabi a daraja. Shin wanda yayi mut'a sau biyar fa?
Allah ka tsare mu da fadawa halaka.

BABI NA BIYU

Muhadu a fitowa ta hudu Insha Allahu Ta'ala.



Ga dukkan mai son shiga ZAUREN FIQHUS SUNNAH, sai ya yi saving wannan number 08142082937 sannan ya aika da cikakken sunansa da adireshinsa.

Comments

Popular posts from this blog

Addu'ar Neman Mijin/Matar Aure

TAMBAYA Assalamu Alaikum warahmatullah malam don Allah ina Neman fatawane Watace take Neman miji kasancewar duk masu  zuwa wurinta ba dagaske suke yi ba toh shi ne ta nemi taimako wurin malamin zaure yake bata rubutu tana sha daniyyar Allah ya sa ta dace. Toh malam abin tambaya anan shi ne shin menene makomar abin da ta aikata? shin malam tayi shirka ne ko kuwa tayi ba daidai ba? nagode. AMSA    Dafarko gameda shan rubutu muddin ayan QUR'ANI ne tsantsa babu wasu zane zanen hatimi, to ya halatta yadda IBN TAIMIYYA ya tabbatar a MAJMU'UL FATAWA, haka ma WAHEED ABDUSSALAM BAALY ya tabbar da hakan a SARIMUL BATTAR,    Amma in akasin haka ne haramun ne don yakan zama shirka ne da surkulle,    Fadin cewa Malamin zaure ne na gargajiya to galibi irin na shirkan sukeyi, don haka ki tuba tsakanin ki da ALLAH da alkawarin bazaki sake zuwa wurin su ba don kare addinin ki da mutuncin ki,    Don samun biyan bukatun ki sai kizage da addu'a da kiyamul...

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI Fitowa na 3

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI               NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 3 (kuma fitowa ta karshe): HAKKOKIN MACE A KAN MIJINTA: Kamar yadda miji yake da hakkoki akan matarsa, haka ita ma matar take da hakkokin akan mijinta, daga cikin wadannan hakkoki akwai : 1 - SADAKI: Hakkin mace ne a bata sadakinta, yayin da za a aure ta, Allah Madaukakin Sarki ya ce: “Ku bawa mata sadakinsu kyauta” (Nisa’i 4). A wani wurin Allah Madaukakin Sarki cewa ya yi:   “Ku aure su da izinin iyalansu, ku basu sadakinsu da adalci” (Addalak : 25). 2 – CIYARWA: Hakkin mata ne akan mijinta ya ciyar da ita, gwargwadon halinsa, koda kuwa tana da wadata da arziki, Allah Madaukakin Sarki yana cewa :  “Mai wadata ya ciyar daga wadatarsa, wanda kuwa aka kuntatawa arzikinsa, to ya ciyar daga abin da Allah ya bashi, Allah baya dorawa wata rai sai abin da ya bata” (Dalaq : 7). An tambayi Manzon Allah, tsira da amincin ...

Hakkokin Ma'aurata a Shari'ar Musulunci Fitowa na 2

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI       NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 2 3 -  YIN ADO DA KWALLIYA: Hakkin miji ne akan matarsa ta yi masa ado da kwalliya, don ta kare shi daga kallon wasu matan daban, wadanda shari’a ta hana shi kallonsu. Mata sun kasance suna kwalliya da dan kunne da awarwaro da munduwa tun a zamanin Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kamar yadda hadisin Abdullahi dan Abbas, Allah Ya kara yarda a gare shi a cikin Sahihul Bukhari da Muslim ya nuna, a lokacin da Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya je wajensu, ya yi musu wa’azi a ranar idi. Kuma saboda Mahimmanci mace ta yi wa mijinta kwalliya, ta zama a shiga mai kyau mai jan hankali, Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya hana miji ya dawo wa iyalinsa daga tafiya cikin dare, ya shigo gida ba tare da sun san da zuwansa ba, An karbo daga Jabir, Allah Ya kara yarda a gare shi, ya ce, Manz...