Skip to main content

MUT'A KO DAI ZINA! Fitowa ta 4

MUT'A KO DAI ZINA!

             Na
Muhammad Umar Ibrahim Gumau

FITOWA TA 4:

BABI NA BIYU

AUREN MUT'A KAFIN YA ZAMO HARAM


Ya kai mai karatu! Allah ya shiryar da mu, shi auren mut'a an haramta shi ne sannu-sannu kamar yadda aka haramta shan giya sannu-sannu. Sannan kuma koda aka halatta yin sa an halattashi ne a halin tafiya, ba a halin zaman gida ba, a lokacin da sahabbai suna wata duniya domin jihadi, sha'awarsu ta yi tsanani, hakurinsu yayi karanci domin sun bar matansu a gida, kuma anaji masu tsoron fitina, kuma gasu suna sababbin musulunta, sai ya kasance daga cikin hikima a cire su daga alfasha sannu-sannu, sai ya zamo yana da hukunci irin na cin mushe ga wanda ya shiga cikin tsanani a wancan lokacin kafin a haramta yinsa.
     
   Domin mai karatu ya san auren mut'a halal ne a farkon al'amari ga wasu Hadisai da suka nuna halaccin yin sa kafin ya zamo haram kuma wadannan Hadisai sune Malaman shi'a suke kafa hujjan halaccin mut'a da su daga littafan Ahlus-sunnah sai su kau da kai daga Hadisan da suke nuni akan haramcin yin sa, ko su karyata su, ko kuma su juyar da hakikanin ma'anar su, domin kawai sun sabawa ra'ayinsu na mut'a.
Ga Hadisan kamar haka:

(1) Daga Abdullahi Dan Mas'ud (R.A) yace: "mun kasance muna yaki tare da Manzon Allah (S.A.W) sai ya saukaka mana mu auri mace da tufafi zuwa wani lokaci".

A wani hadisin na Jabir shima ya ruwaito halaccin auren mut'a.

(2) Daga Jabir Dan Abdullahi da Salamata Dan Ak'wa'i (R.A) sun ce: Me yiwa Manzon Allah (S.A.W) yekuwa ya fito a garemu sai yace "Lallai Manzon Allah (S.A.W) yayi muku izni kuyi mut'a.

(3) Haka kuma a wata ruwayarta Ada'u yace : Jabir Dan Abdullahi yagabato domin Umra, sai muka zo masa a masaukinsa, sai muka tambaye shi game da wasu abubuwa, sannan sai suka ambaci mut'a, sai yace: "E mun yi mut'a zamanin Manzon Allah (S.A.W) da Abubakar da Umar Dan Khattaab".

Shi kuwa wannan hadisin Jabir yana sake jaddada halaccin mut'a kafin haramtuwarta.


Mu hadu a fitowa ta biyar, Insha Allahu Ta'ala.



Ga dukkan mai son shiga ZAUREN FIQHUS SUNNAH, sai ya yi saving wannan number 08142082937 sannan ya aika da cikakken sunansa da adireshinsa.

Comments

Popular posts from this blog

Addu'ar Neman Mijin/Matar Aure

TAMBAYA Assalamu Alaikum warahmatullah malam don Allah ina Neman fatawane Watace take Neman miji kasancewar duk masu  zuwa wurinta ba dagaske suke yi ba toh shi ne ta nemi taimako wurin malamin zaure yake bata rubutu tana sha daniyyar Allah ya sa ta dace. Toh malam abin tambaya anan shi ne shin menene makomar abin da ta aikata? shin malam tayi shirka ne ko kuwa tayi ba daidai ba? nagode. AMSA    Dafarko gameda shan rubutu muddin ayan QUR'ANI ne tsantsa babu wasu zane zanen hatimi, to ya halatta yadda IBN TAIMIYYA ya tabbatar a MAJMU'UL FATAWA, haka ma WAHEED ABDUSSALAM BAALY ya tabbar da hakan a SARIMUL BATTAR,    Amma in akasin haka ne haramun ne don yakan zama shirka ne da surkulle,    Fadin cewa Malamin zaure ne na gargajiya to galibi irin na shirkan sukeyi, don haka ki tuba tsakanin ki da ALLAH da alkawarin bazaki sake zuwa wurin su ba don kare addinin ki da mutuncin ki,    Don samun biyan bukatun ki sai kizage da addu'a da kiyamul...

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI Fitowa na 3

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI               NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 3 (kuma fitowa ta karshe): HAKKOKIN MACE A KAN MIJINTA: Kamar yadda miji yake da hakkoki akan matarsa, haka ita ma matar take da hakkokin akan mijinta, daga cikin wadannan hakkoki akwai : 1 - SADAKI: Hakkin mace ne a bata sadakinta, yayin da za a aure ta, Allah Madaukakin Sarki ya ce: “Ku bawa mata sadakinsu kyauta” (Nisa’i 4). A wani wurin Allah Madaukakin Sarki cewa ya yi:   “Ku aure su da izinin iyalansu, ku basu sadakinsu da adalci” (Addalak : 25). 2 – CIYARWA: Hakkin mata ne akan mijinta ya ciyar da ita, gwargwadon halinsa, koda kuwa tana da wadata da arziki, Allah Madaukakin Sarki yana cewa :  “Mai wadata ya ciyar daga wadatarsa, wanda kuwa aka kuntatawa arzikinsa, to ya ciyar daga abin da Allah ya bashi, Allah baya dorawa wata rai sai abin da ya bata” (Dalaq : 7). An tambayi Manzon Allah, tsira da amincin ...

Hakkokin Ma'aurata a Shari'ar Musulunci Fitowa na 2

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI       NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 2 3 -  YIN ADO DA KWALLIYA: Hakkin miji ne akan matarsa ta yi masa ado da kwalliya, don ta kare shi daga kallon wasu matan daban, wadanda shari’a ta hana shi kallonsu. Mata sun kasance suna kwalliya da dan kunne da awarwaro da munduwa tun a zamanin Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kamar yadda hadisin Abdullahi dan Abbas, Allah Ya kara yarda a gare shi a cikin Sahihul Bukhari da Muslim ya nuna, a lokacin da Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya je wajensu, ya yi musu wa’azi a ranar idi. Kuma saboda Mahimmanci mace ta yi wa mijinta kwalliya, ta zama a shiga mai kyau mai jan hankali, Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya hana miji ya dawo wa iyalinsa daga tafiya cikin dare, ya shigo gida ba tare da sun san da zuwansa ba, An karbo daga Jabir, Allah Ya kara yarda a gare shi, ya ce, Manz...