Skip to main content

MUT'A KO DAI ZINA! Fitowa ta 5

MUT'A KO DAI ZINA!

             Na
Muhammad Umar Ibrahim Gumau

FITOWA TA 5:

BABI NA BIYU

AUREN MUT'A KAFIN YA ZAMO HARAM


(4) An karbo daga Jabir Dan Abdullahi (R.A) yace: Mun kasance muna mut'a da damkar tafi na Dabino da Gari na wasu kwanaki a zamanin Manzon Allah (S.A.W) har Umar Dan Khattaab ya yi hani daga gare shi.

Wannan Hadisi na hudu wato hadisin Jabir yana daga cikin hadisan da 'yan shi'a suke jefa shubuhar su ga jahilai, saboda cewar da Jabir Dan Abdullahi yayi: (Mun kasance muna mut'a a zamanin Manzon Allah (S.A.W) da Abubakar da Umar Dan Khattaab......) Imamun Nawawi ya warware shubuhar, yana cewa:

  "Amma dalilin su daga Hadisin Jabir Dan Abdullahi (R.A) da yace: Munyi mut'a  a zamanin Manzon Allah (S.A.W) da Abubakar da Umar Dan Khattaab...,  za'a dauki wannan  ne akan cewa wadanda suka yi mut'a a zamanin Abubakar da wani yanki na halifancin Umar Dan Khattaab, labarin haramcin yin haka bai je gare su ba, daga cikinsu akwai shi kansa Jabir (R.A).

Wadannan sune kadan daga Hadisan da suka nuna halaccin auren mut'a kafin haramtuwar sa, saboda haka ne Malaman sunnah suka yi ijma'i akan halaccin auren mut'a a farkon musulunci na wasu kwanaki 'yan kadan kafin Manzon Allah (S.A.W) ya haramta shi haramci na har abada, kuma Wadannan hadisai babu shakka an shafe hukuncinsu da hadisan da suka haramta auren mut'a, kamar yadda Insha Allahu mai karatu zai gansu nan gaba kadan.


 ABUBUWAN DA MAI KARATU ZAI FAHIMTA DAGA WADANNAN HADISAI:-

1- ba a halatta musu ba sai a halin tafiya.
2- Sun bar matan su a gida
3- Sha'awar su tayi tsanani.
4- Ana ji musu tsoron fadawa cikin fitina.
5- Halaccin na wani lokaci ne da bai wuce kwana uku ba.
6- Wadanda suka yi mut'a a zamanin Abubakar da wani yanki na halifancin Umar Dan Khattaab hanin bai kai garesu ba, daga cikin su akwai shi kansa Jabir Dan Abdullahi (R.A)
7- Tsanani ya sa aka halatta musu, saboda haka yake da hukuncin cin mushe ga wanda ya shiga tsanani a wancan lokacin.


   MAKIRCIN SHI'A A CIKIN WADANNAN HADISAI

Rashin yiwa mabiya irin wannan bayanai domin kada su fahimci gaskiya.



Mu hadu a fitowa ta shida, Insha Allahu Ta'ala.



Ga dukkan mai son shiga ZAUREN FIQHUS SUNNAH, sai ya yi saving wannan number 08142082937 sannan ya aika da cikakken sunansa da adireshinsa.

Comments

Popular posts from this blog

Addu'ar Neman Mijin/Matar Aure

TAMBAYA Assalamu Alaikum warahmatullah malam don Allah ina Neman fatawane Watace take Neman miji kasancewar duk masu  zuwa wurinta ba dagaske suke yi ba toh shi ne ta nemi taimako wurin malamin zaure yake bata rubutu tana sha daniyyar Allah ya sa ta dace. Toh malam abin tambaya anan shi ne shin menene makomar abin da ta aikata? shin malam tayi shirka ne ko kuwa tayi ba daidai ba? nagode. AMSA    Dafarko gameda shan rubutu muddin ayan QUR'ANI ne tsantsa babu wasu zane zanen hatimi, to ya halatta yadda IBN TAIMIYYA ya tabbatar a MAJMU'UL FATAWA, haka ma WAHEED ABDUSSALAM BAALY ya tabbar da hakan a SARIMUL BATTAR,    Amma in akasin haka ne haramun ne don yakan zama shirka ne da surkulle,    Fadin cewa Malamin zaure ne na gargajiya to galibi irin na shirkan sukeyi, don haka ki tuba tsakanin ki da ALLAH da alkawarin bazaki sake zuwa wurin su ba don kare addinin ki da mutuncin ki,    Don samun biyan bukatun ki sai kizage da addu'a da kiyamul...

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI Fitowa na 3

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI               NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 3 (kuma fitowa ta karshe): HAKKOKIN MACE A KAN MIJINTA: Kamar yadda miji yake da hakkoki akan matarsa, haka ita ma matar take da hakkokin akan mijinta, daga cikin wadannan hakkoki akwai : 1 - SADAKI: Hakkin mace ne a bata sadakinta, yayin da za a aure ta, Allah Madaukakin Sarki ya ce: “Ku bawa mata sadakinsu kyauta” (Nisa’i 4). A wani wurin Allah Madaukakin Sarki cewa ya yi:   “Ku aure su da izinin iyalansu, ku basu sadakinsu da adalci” (Addalak : 25). 2 – CIYARWA: Hakkin mata ne akan mijinta ya ciyar da ita, gwargwadon halinsa, koda kuwa tana da wadata da arziki, Allah Madaukakin Sarki yana cewa :  “Mai wadata ya ciyar daga wadatarsa, wanda kuwa aka kuntatawa arzikinsa, to ya ciyar daga abin da Allah ya bashi, Allah baya dorawa wata rai sai abin da ya bata” (Dalaq : 7). An tambayi Manzon Allah, tsira da amincin ...

Hakkokin Ma'aurata a Shari'ar Musulunci Fitowa na 2

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI       NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 2 3 -  YIN ADO DA KWALLIYA: Hakkin miji ne akan matarsa ta yi masa ado da kwalliya, don ta kare shi daga kallon wasu matan daban, wadanda shari’a ta hana shi kallonsu. Mata sun kasance suna kwalliya da dan kunne da awarwaro da munduwa tun a zamanin Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kamar yadda hadisin Abdullahi dan Abbas, Allah Ya kara yarda a gare shi a cikin Sahihul Bukhari da Muslim ya nuna, a lokacin da Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya je wajensu, ya yi musu wa’azi a ranar idi. Kuma saboda Mahimmanci mace ta yi wa mijinta kwalliya, ta zama a shiga mai kyau mai jan hankali, Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya hana miji ya dawo wa iyalinsa daga tafiya cikin dare, ya shigo gida ba tare da sun san da zuwansa ba, An karbo daga Jabir, Allah Ya kara yarda a gare shi, ya ce, Manz...