Skip to main content

YANDA AKE SALLAN KISFEWAR RANA KO WATA A TAKAICE

YANDA AKE SALLAN KISFEWAR RANA KO WATA A TAKAICE:


KIRAN JAMA'A:
Za a rinka maimaitawa kalmar "Assalatu Jaami'ah"  har sai an tabbatar da jama'a sun ji, saboda hadisin Abdullahi Bn Amru dake cikin Bukhari da Muslim.

YANDA AKE YIN TA:

 Raka'o'i ne guda biyu a kowace raka'a akwai tsayuwa biyu, da karatu biyu da ruku'u biyu da sujada biyu; ga bayaninsu kamar haka:

 Raka'an farko liman zai kabbara ba tare da an tayar da iqama ba, sannan ya karanta fatiha da sura mai tsaho, sannan ya yi ruku'u mai tsaho, sannan ya dago daga ruku'u sai ya karanta fatiha da sura mai tsaho, amma kai ta kai na farko tsayi, sannan ya sake ruku'u mai tsaho amma kar ya kai tsayin ruku'u na farko, sannan ya dago daga ruku'u sai ya tafi sujada mai tsaho, sannan idan ya dago daga sujada sai ya sake komawa sujada mai tsaho amma karta kai na farko tsayi, sannan sai ya sake mikewa. Ya samu raka'a daya kenan, kuma haka zai maimaita a raka'a ta biyu.

Wannan shi ne bayani a takaice kamar yanda ya zo a hadisin Nana A'isha, Allah Ta'ala Ya kara yarda a gare ta, dake cikin littafin Sahihu Muslim.

Sannan yana daga cikin Sunnah idan an kammala wannan sallah, Limami ya umurci mutane da yawaita addu'a, tuba, da neman gafaran Allah Ta'ala. Kamar yanda Ya zo a cikin littafin Sahihul Bukhari.

Allah Ta'ala Ya sa mu dace.

Dan uwanku a Musulunci:
Umar Shehu Zaria

ZAUREN FIQHUS SUNNAH 08034666220

Comments

Popular posts from this blog

Addu'ar Neman Mijin/Matar Aure

TAMBAYA Assalamu Alaikum warahmatullah malam don Allah ina Neman fatawane Watace take Neman miji kasancewar duk masu  zuwa wurinta ba dagaske suke yi ba toh shi ne ta nemi taimako wurin malamin zaure yake bata rubutu tana sha daniyyar Allah ya sa ta dace. Toh malam abin tambaya anan shi ne shin menene makomar abin da ta aikata? shin malam tayi shirka ne ko kuwa tayi ba daidai ba? nagode. AMSA    Dafarko gameda shan rubutu muddin ayan QUR'ANI ne tsantsa babu wasu zane zanen hatimi, to ya halatta yadda IBN TAIMIYYA ya tabbatar a MAJMU'UL FATAWA, haka ma WAHEED ABDUSSALAM BAALY ya tabbar da hakan a SARIMUL BATTAR,    Amma in akasin haka ne haramun ne don yakan zama shirka ne da surkulle,    Fadin cewa Malamin zaure ne na gargajiya to galibi irin na shirkan sukeyi, don haka ki tuba tsakanin ki da ALLAH da alkawarin bazaki sake zuwa wurin su ba don kare addinin ki da mutuncin ki,    Don samun biyan bukatun ki sai kizage da addu'a da kiyamul...

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI Fitowa na 3

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI               NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 3 (kuma fitowa ta karshe): HAKKOKIN MACE A KAN MIJINTA: Kamar yadda miji yake da hakkoki akan matarsa, haka ita ma matar take da hakkokin akan mijinta, daga cikin wadannan hakkoki akwai : 1 - SADAKI: Hakkin mace ne a bata sadakinta, yayin da za a aure ta, Allah Madaukakin Sarki ya ce: “Ku bawa mata sadakinsu kyauta” (Nisa’i 4). A wani wurin Allah Madaukakin Sarki cewa ya yi:   “Ku aure su da izinin iyalansu, ku basu sadakinsu da adalci” (Addalak : 25). 2 – CIYARWA: Hakkin mata ne akan mijinta ya ciyar da ita, gwargwadon halinsa, koda kuwa tana da wadata da arziki, Allah Madaukakin Sarki yana cewa :  “Mai wadata ya ciyar daga wadatarsa, wanda kuwa aka kuntatawa arzikinsa, to ya ciyar daga abin da Allah ya bashi, Allah baya dorawa wata rai sai abin da ya bata” (Dalaq : 7). An tambayi Manzon Allah, tsira da amincin ...

Hakkokin Ma'aurata a Shari'ar Musulunci Fitowa na 2

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI       NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 2 3 -  YIN ADO DA KWALLIYA: Hakkin miji ne akan matarsa ta yi masa ado da kwalliya, don ta kare shi daga kallon wasu matan daban, wadanda shari’a ta hana shi kallonsu. Mata sun kasance suna kwalliya da dan kunne da awarwaro da munduwa tun a zamanin Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kamar yadda hadisin Abdullahi dan Abbas, Allah Ya kara yarda a gare shi a cikin Sahihul Bukhari da Muslim ya nuna, a lokacin da Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya je wajensu, ya yi musu wa’azi a ranar idi. Kuma saboda Mahimmanci mace ta yi wa mijinta kwalliya, ta zama a shiga mai kyau mai jan hankali, Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya hana miji ya dawo wa iyalinsa daga tafiya cikin dare, ya shigo gida ba tare da sun san da zuwansa ba, An karbo daga Jabir, Allah Ya kara yarda a gare shi, ya ce, Manz...