Skip to main content

Hukuncin Sallah kan mashayin giya...

Assalamu Alaikum.
To Allah ya gafarta malam, wanda ya san wajibcin sallah da azumi akansa amma saboda ya taba jin fatawar cewa duk wanda yasha giya sai yayi kwana 40 ba'a ansar ibadar sa shi kuma baya kwana 40 baisha giya ba sai yabar sallah da azumi tsawon shekaru, yanzu kuma ya tuba ya bari ya ramuwar sallar da azumin da yabari zai kasance?

Wa'alaikumussalam

Amsa

Lallai hadisai sun nuna ba'a karbar sallar wanda ya sha giya ta kwana arba'in kamar yadda yazo cikin silsilah swahiha 709, hadisin ya nuna idan mutun ya tuba Allah zai yafe masa, saboda haka tunda ya tuba muna fatar Allah zai yafe masa, sai yaci gaba da istigfari da yawaita ibada,
Malamai sunyi sabani wajen ramakon sallah da azumi ga wanda yabar su baiyi har tsawo wani lokaci,  wasu sunce zai rama wannan shine ra'ayin Jamhurun malamai  waau kuma sunce ba zai rama ba don sun gina fahimtar su akan dalilai na shari'a da suka nuna kafurcin wanda yabar sallah, sannan suka ce in ance zai ya rama hakan ka iya wahalar dashi kila ya kasa ya koma gidan jiya,  suna hujja kuma da fadar cikin Suratul Ɗaha 11, da ta 82.
Don haka dai babu ramuwa akan sa sai istigfari da tsaida sallah da ci gaba da azumi da lazimtar ibada sosai da sosai, an tambayi malaman  lajna 6/41 hukuncin wanda yabar sallah da azumi sun bada fatawar ba zai rama ba.

Wallahu A'alam.

Malam Nuruddeen Muhammad Mujaheed

07/08/2016.

Daga : ZAUREN FIQHUS SUNNAH group.

Comments

Popular posts from this blog

Addu'ar Neman Mijin/Matar Aure

TAMBAYA Assalamu Alaikum warahmatullah malam don Allah ina Neman fatawane Watace take Neman miji kasancewar duk masu  zuwa wurinta ba dagaske suke yi ba toh shi ne ta nemi taimako wurin malamin zaure yake bata rubutu tana sha daniyyar Allah ya sa ta dace. Toh malam abin tambaya anan shi ne shin menene makomar abin da ta aikata? shin malam tayi shirka ne ko kuwa tayi ba daidai ba? nagode. AMSA    Dafarko gameda shan rubutu muddin ayan QUR'ANI ne tsantsa babu wasu zane zanen hatimi, to ya halatta yadda IBN TAIMIYYA ya tabbatar a MAJMU'UL FATAWA, haka ma WAHEED ABDUSSALAM BAALY ya tabbar da hakan a SARIMUL BATTAR,    Amma in akasin haka ne haramun ne don yakan zama shirka ne da surkulle,    Fadin cewa Malamin zaure ne na gargajiya to galibi irin na shirkan sukeyi, don haka ki tuba tsakanin ki da ALLAH da alkawarin bazaki sake zuwa wurin su ba don kare addinin ki da mutuncin ki,    Don samun biyan bukatun ki sai kizage da addu'a da kiyamul...

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI Fitowa na 3

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI               NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 3 (kuma fitowa ta karshe): HAKKOKIN MACE A KAN MIJINTA: Kamar yadda miji yake da hakkoki akan matarsa, haka ita ma matar take da hakkokin akan mijinta, daga cikin wadannan hakkoki akwai : 1 - SADAKI: Hakkin mace ne a bata sadakinta, yayin da za a aure ta, Allah Madaukakin Sarki ya ce: “Ku bawa mata sadakinsu kyauta” (Nisa’i 4). A wani wurin Allah Madaukakin Sarki cewa ya yi:   “Ku aure su da izinin iyalansu, ku basu sadakinsu da adalci” (Addalak : 25). 2 – CIYARWA: Hakkin mata ne akan mijinta ya ciyar da ita, gwargwadon halinsa, koda kuwa tana da wadata da arziki, Allah Madaukakin Sarki yana cewa :  “Mai wadata ya ciyar daga wadatarsa, wanda kuwa aka kuntatawa arzikinsa, to ya ciyar daga abin da Allah ya bashi, Allah baya dorawa wata rai sai abin da ya bata” (Dalaq : 7). An tambayi Manzon Allah, tsira da amincin ...

Hakkokin Ma'aurata a Shari'ar Musulunci Fitowa na 2

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI       NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 2 3 -  YIN ADO DA KWALLIYA: Hakkin miji ne akan matarsa ta yi masa ado da kwalliya, don ta kare shi daga kallon wasu matan daban, wadanda shari’a ta hana shi kallonsu. Mata sun kasance suna kwalliya da dan kunne da awarwaro da munduwa tun a zamanin Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kamar yadda hadisin Abdullahi dan Abbas, Allah Ya kara yarda a gare shi a cikin Sahihul Bukhari da Muslim ya nuna, a lokacin da Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya je wajensu, ya yi musu wa’azi a ranar idi. Kuma saboda Mahimmanci mace ta yi wa mijinta kwalliya, ta zama a shiga mai kyau mai jan hankali, Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya hana miji ya dawo wa iyalinsa daga tafiya cikin dare, ya shigo gida ba tare da sun san da zuwansa ba, An karbo daga Jabir, Allah Ya kara yarda a gare shi, ya ce, Manz...