Skip to main content

KU YI HATTARA MATA KUNE FA IYAYEN AL'UMMA

Tabbas mata mutane ne masu mutumci ba mai mutumta su sai mutum mai mutumci, kuma ba mai wulakanta su sai wulakantacce. Annabi (saw) ya mana wasiyya a ranar Hajjin ban kwana kan tausasawa mata, da kuma umarni ga maza da mta su kula da hakkin junan su.
To 'yan uwa na maza da mata mu sani yana daga hakkin iyalan mu akan mu lallai mu kula da tarbiyyar su, sannna a junan mu musulmai muna yiwa juna nasiha,  bisa wannan nake tuna mana cewa: Allah yayi umarni ga Annabi (saw) da ya gayawa matansa, da 'ya 'yansa, da sauran mata muminai kcewa in zasu fita su sanya sutura isash-shi ya da zata rufe masu dukkan jiki. Anan kada mu bari al'adun mu, ko zamani ko tasirin wayewa yasa mu manta da umarnin Allah dana manzon Allah yayin sanya suturar mu.
Shifa bawa mabukaci ne a gun Allah, kuma ba sai lokacin bukatar mu a gun Allah ba, ko yayin wani taro na addini, ko yayin jana'iza ko in za'a je ta'aziyya, ko ranar sallah ko a haduwar junan mu zamu yiwa Allah da'a ta sanya suturar da aka umarce mu ba.
Na kan ga 'yan uwa mata yayin bukukuwa, ko a manyan makarantu, ko in sunyi nesa da gida, ko ofisoshi suna sa6awa Allah wajen tufafi da yakamata su saka... Lallai wannan babban laifi ne. Mu Sani a ko ina muke Allah yana ganin mu, kuma kowa a lahira da aikin sa za'a masa hisabi, muji tsoron Allah bamu san akan wacce ga6a zamu bar duniya ba..
Lallai iyaye, malami da shugabanni ku tsaya kan al'ummar mu da nusar damu kan tsarin suturar da wassu matan mu na yau ke sawa in zasu bayyana a gaban jama'ar da bai halatta su gansu da irin wannan tufafi ba.
Hakika bayyana tsiraici haramun ne, kuma yana haifar da matsaloli da yawa. Allah ya hana fita irin ta kafirai, da sanya matsats-tun tufafi, da son yin kama da maza, ko koyi da arna.
Matan dake bayyana tsiraici basa tsoron gamuwa da fushi Allah, ko tunanin hatsarin gamuwa da shafar aljanu, mu sani fa 'yan uwa mata bayyana jiki yana jawo raguwar imani da zubewar mutumci, da bushewar zuciya da karancin kunya, kuma zuriyar ku zasu iya gadon wannan mugun aiki, hakanan al'umma na iya koyi daku.
Allah mai rahama mai jin kai muna rokon ka shiryar da iyalan mu, Ka sanya matan al'umar mu manya da yara suna sanya sutura wanda ka yarda da ita, Allah ka yafe masu kura-kuran su, ka sanya kwadayin rahamar ka a zukatan su, ka tsare su daga fizga daga shaidan.
Mata ku sani kune iyayen al'umma kuma kune makarantar farko ga 'ya 'yan ku. To fa ance in bishiya ta karkace bata bada mikakkiyar inuwa.... Muna fatan ku zama na kwarai al'umar mu su taso a hannun mata  masu nagarta.

Daga:
Sheikh Aliyu Sa'id Gamawa

Comments

Popular posts from this blog

Addu'ar Neman Mijin/Matar Aure

TAMBAYA Assalamu Alaikum warahmatullah malam don Allah ina Neman fatawane Watace take Neman miji kasancewar duk masu  zuwa wurinta ba dagaske suke yi ba toh shi ne ta nemi taimako wurin malamin zaure yake bata rubutu tana sha daniyyar Allah ya sa ta dace. Toh malam abin tambaya anan shi ne shin menene makomar abin da ta aikata? shin malam tayi shirka ne ko kuwa tayi ba daidai ba? nagode. AMSA    Dafarko gameda shan rubutu muddin ayan QUR'ANI ne tsantsa babu wasu zane zanen hatimi, to ya halatta yadda IBN TAIMIYYA ya tabbatar a MAJMU'UL FATAWA, haka ma WAHEED ABDUSSALAM BAALY ya tabbar da hakan a SARIMUL BATTAR,    Amma in akasin haka ne haramun ne don yakan zama shirka ne da surkulle,    Fadin cewa Malamin zaure ne na gargajiya to galibi irin na shirkan sukeyi, don haka ki tuba tsakanin ki da ALLAH da alkawarin bazaki sake zuwa wurin su ba don kare addinin ki da mutuncin ki,    Don samun biyan bukatun ki sai kizage da addu'a da kiyamul...

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI Fitowa na 3

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI               NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 3 (kuma fitowa ta karshe): HAKKOKIN MACE A KAN MIJINTA: Kamar yadda miji yake da hakkoki akan matarsa, haka ita ma matar take da hakkokin akan mijinta, daga cikin wadannan hakkoki akwai : 1 - SADAKI: Hakkin mace ne a bata sadakinta, yayin da za a aure ta, Allah Madaukakin Sarki ya ce: “Ku bawa mata sadakinsu kyauta” (Nisa’i 4). A wani wurin Allah Madaukakin Sarki cewa ya yi:   “Ku aure su da izinin iyalansu, ku basu sadakinsu da adalci” (Addalak : 25). 2 – CIYARWA: Hakkin mata ne akan mijinta ya ciyar da ita, gwargwadon halinsa, koda kuwa tana da wadata da arziki, Allah Madaukakin Sarki yana cewa :  “Mai wadata ya ciyar daga wadatarsa, wanda kuwa aka kuntatawa arzikinsa, to ya ciyar daga abin da Allah ya bashi, Allah baya dorawa wata rai sai abin da ya bata” (Dalaq : 7). An tambayi Manzon Allah, tsira da amincin ...

Hakkokin Ma'aurata a Shari'ar Musulunci Fitowa na 2

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI       NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 2 3 -  YIN ADO DA KWALLIYA: Hakkin miji ne akan matarsa ta yi masa ado da kwalliya, don ta kare shi daga kallon wasu matan daban, wadanda shari’a ta hana shi kallonsu. Mata sun kasance suna kwalliya da dan kunne da awarwaro da munduwa tun a zamanin Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kamar yadda hadisin Abdullahi dan Abbas, Allah Ya kara yarda a gare shi a cikin Sahihul Bukhari da Muslim ya nuna, a lokacin da Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya je wajensu, ya yi musu wa’azi a ranar idi. Kuma saboda Mahimmanci mace ta yi wa mijinta kwalliya, ta zama a shiga mai kyau mai jan hankali, Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya hana miji ya dawo wa iyalinsa daga tafiya cikin dare, ya shigo gida ba tare da sun san da zuwansa ba, An karbo daga Jabir, Allah Ya kara yarda a gare shi, ya ce, Manz...