Skip to main content

HUKUNCIN HULDA DA YAHUDU DA NASARA !!

Tambaya

Assalaamu alaikum.
Allah ya qarawa Dakta lafiya, don Allah ina son amsar tambayoyin nan tare da hujja don gamsar da abokan karatuna.
1. Minene matsayin amsa gayyatar chiristoci zuwa cikin choci don wani taro da suke yi na graduation ko makamancin haka amma a cikin choci?
2. Minene matsayin shiga choci din karan-kansa?
3. Menene matsayin fara yiwa wanda ba musulmi ba sallama ?

Allah ya qarawa mallam ikhlasi da ilimi mai amfani

Amsa

Wa alaikum assalam, Annabi (SAW) ya hana fara yiwa CRISTER sallama kamar yadda ya zo a hadisin Tirmizi.

Ya halatta Musulmi ya yi hulda da Crister ya kuma kyautata masa in har ana zaune lafiya , kamar yadda aya ta (8) a suratul Mumtahanah ta tabbatar da hakan, sannan zai iya cin yankansa kamar yadda aya ta (5) a suratul Ma'idah ta yi bayanin hakan.
Annabi (SAW) ya rasu silkensa na yaki yana wajan Bayahude, saboda ya amshi abincin da za'a ci a gidansa, sannan da aka bude Khaibar ya bar gonakin musulmai a wajan Yadudawa sun rinka nomawa suna bawa musulmai wani kaso kamar yadda Bukhari ya rawaito a Sahihinsa

Nasaran Najran sun zo wajan Annabi SAW ya sauke su a Masallaci, sannan   ya  zo a Musannaf a lamba ta: (4871) cewa: " Sahabin manzon Allah Abu-Musa Al'ash'ary ya taba yin sallah a wata coci da ake cewa NAHYA a Damshk lokacin da bai samu  masallacin ba.

Tarurrukan Kristoci ba sa rabuwa da kade-kade da raye-raye da cakuduwa tsakanin maza da mata, ga kuma manyan hotuna a like a bango, wannan yasa rashin halartar taronsu shi ne daidai, saboda gujewa keta iyakokin Allah.

Allah ne mafi sani

Dr. Jamilu Zarewa

13/09/2018

Daga ZAUREN FIQHUS SUNNAH

Comments

Popular posts from this blog

Addu'ar Neman Mijin/Matar Aure

TAMBAYA Assalamu Alaikum warahmatullah malam don Allah ina Neman fatawane Watace take Neman miji kasancewar duk masu  zuwa wurinta ba dagaske suke yi ba toh shi ne ta nemi taimako wurin malamin zaure yake bata rubutu tana sha daniyyar Allah ya sa ta dace. Toh malam abin tambaya anan shi ne shin menene makomar abin da ta aikata? shin malam tayi shirka ne ko kuwa tayi ba daidai ba? nagode. AMSA    Dafarko gameda shan rubutu muddin ayan QUR'ANI ne tsantsa babu wasu zane zanen hatimi, to ya halatta yadda IBN TAIMIYYA ya tabbatar a MAJMU'UL FATAWA, haka ma WAHEED ABDUSSALAM BAALY ya tabbar da hakan a SARIMUL BATTAR,    Amma in akasin haka ne haramun ne don yakan zama shirka ne da surkulle,    Fadin cewa Malamin zaure ne na gargajiya to galibi irin na shirkan sukeyi, don haka ki tuba tsakanin ki da ALLAH da alkawarin bazaki sake zuwa wurin su ba don kare addinin ki da mutuncin ki,    Don samun biyan bukatun ki sai kizage da addu'a da kiyamul...

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI Fitowa na 3

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI               NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 3 (kuma fitowa ta karshe): HAKKOKIN MACE A KAN MIJINTA: Kamar yadda miji yake da hakkoki akan matarsa, haka ita ma matar take da hakkokin akan mijinta, daga cikin wadannan hakkoki akwai : 1 - SADAKI: Hakkin mace ne a bata sadakinta, yayin da za a aure ta, Allah Madaukakin Sarki ya ce: “Ku bawa mata sadakinsu kyauta” (Nisa’i 4). A wani wurin Allah Madaukakin Sarki cewa ya yi:   “Ku aure su da izinin iyalansu, ku basu sadakinsu da adalci” (Addalak : 25). 2 – CIYARWA: Hakkin mata ne akan mijinta ya ciyar da ita, gwargwadon halinsa, koda kuwa tana da wadata da arziki, Allah Madaukakin Sarki yana cewa :  “Mai wadata ya ciyar daga wadatarsa, wanda kuwa aka kuntatawa arzikinsa, to ya ciyar daga abin da Allah ya bashi, Allah baya dorawa wata rai sai abin da ya bata” (Dalaq : 7). An tambayi Manzon Allah, tsira da amincin ...

Hakkokin Ma'aurata a Shari'ar Musulunci Fitowa na 2

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI       NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 2 3 -  YIN ADO DA KWALLIYA: Hakkin miji ne akan matarsa ta yi masa ado da kwalliya, don ta kare shi daga kallon wasu matan daban, wadanda shari’a ta hana shi kallonsu. Mata sun kasance suna kwalliya da dan kunne da awarwaro da munduwa tun a zamanin Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kamar yadda hadisin Abdullahi dan Abbas, Allah Ya kara yarda a gare shi a cikin Sahihul Bukhari da Muslim ya nuna, a lokacin da Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya je wajensu, ya yi musu wa’azi a ranar idi. Kuma saboda Mahimmanci mace ta yi wa mijinta kwalliya, ta zama a shiga mai kyau mai jan hankali, Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya hana miji ya dawo wa iyalinsa daga tafiya cikin dare, ya shigo gida ba tare da sun san da zuwansa ba, An karbo daga Jabir, Allah Ya kara yarda a gare shi, ya ce, Manz...