Skip to main content

IDAN AKA SAMU RIKITA-RIKITA A WAJAN SAKI, ZUWA KOTU SHI NE MAFITA !!

Tambaya

Assalamu'Alaikum wa Rahmatullahi wa Barakatuh! Don Allah Mallam ina fatawa akan batun Auren yarinyar da Mijinta suka samu matsala har ta kai ga ta koma gida akan cewa ba ta son shi.
A takaice dai mijin da yaje gidan su, ya tambayeta akan 'yanzu me take so'? Sai tace masa ita rabuwa take so su yi, Sai yace mata to kije mun rabu, Kuma gobe kafin karfe 10 na safe ki zo ki kwashe kayanki, Kuma ki bada 'yata a kawo min, Sai ta ce da shi ai a rubuce ake yi, sai yace mata, ai sanda aka daura auren ba'a ce ya rubuta ba, saboda haka yanzu ma ba sai ya rubuta ba. Bayan anyi haka, sunje  kwashe kaya sai yace ai shi bai ce ya sake ta ba. Har sai da lamarin ya kai ta matsa masa akan takardar, sai ya rubuta cewa" Ni wane na saki matata saki daya, amma na maida ita"
Mallam sai tace masa ai ba'a rubuta haka Saidai ya rubuta sakin kawai.. amma maidawar Sai ya zo daga baya a furuci kawai. Sai ya karbi wannan takardar ya yaga ya sake rubuta wata, cewa yayi saki daya, a bisa sharadin in yayi hakan za ta koma? Tace da shi za ta koma. To amma bayan ya rubuta sai Ta ce ita wallahi ba zata koma ba. Shi kuma mijin yace ya maida ta, ita kuma ta ce wallahi ba za ta komaba koda ko zata mutu ne.
Malam tace ita aurenshi ya zamo mata wani abin al'ajabi don ba ta taba jin sonsa a ranta ba ko da da kwayar zarra ne a  ranta. saboda munanan halayensa sun sa ba ta iya yi masa biyayya ko kadan. Kuma tace ba zata taba iya yin hakan ba. Don haka sai take ganin hanyar halaka ce suka kama dukkansu. Don haka ita bazata iya komawa ba, Shi kuma yace halayensa da basu da kyau babu wanda ya isa yasa shi ya canza, koda ko mahaifiyar sa ce da mahaifin sa, malam yana neman mata, da tayi magana sai yace mata wallahi yanzu ya soma. Wai meyasa iyayenta ba su yi bincikeba tun farko, suka daura musu auren?

Don Allah Malam menene mafita anan? Yanzu haka saboda bakin cikin lamarin , tana nan a kwance ba lafiya.

Amsa
Wa alaikumus salam
Sakin mace da baki yana daidai da sakinta a rubuce, magana ma tafi rubutu karfi a shariance, don haka ta saku tun furuncinsa na farko.

Idan miji ya saki matarsa saki daya yana da damar da zai mata kome mutukar ba ta gama idda ba, kuma iyayen matar ko ita kanta ba su da damar da za su ja masa birki kamar yadda aya ta (228) a suratul Bakara ta tabbatar da hakan.

Idan bangaren amarya da Ango suka jaa daaga aka kasa samun matsaya, zuwa kotu shi ne maslaha, fatawa ba za ta yi tasiri ba, saboda alkali yana da karfin hukuma, malami kuma aikinsa bada hukuncin Allah kawai, wannan yasa nake baku shawarar zuwa kotu don ta warware muku rikicin da kuke ciki.

Ya halatta mace ta nemi saki idan ya zamanto akwai cutarwa tsakaninta da mijinta ko kuma ba za ta iya tsayawa da hakkokinsa ba, kamar yadda kissar Thabit bn Kais bn Shammas da matarsa Jamila ta tabbatar da hakan a hadisai ingantattu.

Allah ne mafi sani

Dr. Jamilu Zarewa

12/09/2018

Daga ZAUREN FIQHUS SUNNAH

Comments

Popular posts from this blog

Addu'ar Neman Mijin/Matar Aure

TAMBAYA Assalamu Alaikum warahmatullah malam don Allah ina Neman fatawane Watace take Neman miji kasancewar duk masu  zuwa wurinta ba dagaske suke yi ba toh shi ne ta nemi taimako wurin malamin zaure yake bata rubutu tana sha daniyyar Allah ya sa ta dace. Toh malam abin tambaya anan shi ne shin menene makomar abin da ta aikata? shin malam tayi shirka ne ko kuwa tayi ba daidai ba? nagode. AMSA    Dafarko gameda shan rubutu muddin ayan QUR'ANI ne tsantsa babu wasu zane zanen hatimi, to ya halatta yadda IBN TAIMIYYA ya tabbatar a MAJMU'UL FATAWA, haka ma WAHEED ABDUSSALAM BAALY ya tabbar da hakan a SARIMUL BATTAR,    Amma in akasin haka ne haramun ne don yakan zama shirka ne da surkulle,    Fadin cewa Malamin zaure ne na gargajiya to galibi irin na shirkan sukeyi, don haka ki tuba tsakanin ki da ALLAH da alkawarin bazaki sake zuwa wurin su ba don kare addinin ki da mutuncin ki,    Don samun biyan bukatun ki sai kizage da addu'a da kiyamul...

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI Fitowa na 3

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI               NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 3 (kuma fitowa ta karshe): HAKKOKIN MACE A KAN MIJINTA: Kamar yadda miji yake da hakkoki akan matarsa, haka ita ma matar take da hakkokin akan mijinta, daga cikin wadannan hakkoki akwai : 1 - SADAKI: Hakkin mace ne a bata sadakinta, yayin da za a aure ta, Allah Madaukakin Sarki ya ce: “Ku bawa mata sadakinsu kyauta” (Nisa’i 4). A wani wurin Allah Madaukakin Sarki cewa ya yi:   “Ku aure su da izinin iyalansu, ku basu sadakinsu da adalci” (Addalak : 25). 2 – CIYARWA: Hakkin mata ne akan mijinta ya ciyar da ita, gwargwadon halinsa, koda kuwa tana da wadata da arziki, Allah Madaukakin Sarki yana cewa :  “Mai wadata ya ciyar daga wadatarsa, wanda kuwa aka kuntatawa arzikinsa, to ya ciyar daga abin da Allah ya bashi, Allah baya dorawa wata rai sai abin da ya bata” (Dalaq : 7). An tambayi Manzon Allah, tsira da amincin ...

Hakkokin Ma'aurata a Shari'ar Musulunci Fitowa na 2

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI       NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 2 3 -  YIN ADO DA KWALLIYA: Hakkin miji ne akan matarsa ta yi masa ado da kwalliya, don ta kare shi daga kallon wasu matan daban, wadanda shari’a ta hana shi kallonsu. Mata sun kasance suna kwalliya da dan kunne da awarwaro da munduwa tun a zamanin Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kamar yadda hadisin Abdullahi dan Abbas, Allah Ya kara yarda a gare shi a cikin Sahihul Bukhari da Muslim ya nuna, a lokacin da Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya je wajensu, ya yi musu wa’azi a ranar idi. Kuma saboda Mahimmanci mace ta yi wa mijinta kwalliya, ta zama a shiga mai kyau mai jan hankali, Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya hana miji ya dawo wa iyalinsa daga tafiya cikin dare, ya shigo gida ba tare da sun san da zuwansa ba, An karbo daga Jabir, Allah Ya kara yarda a gare shi, ya ce, Manz...