Wallafar: Shaik Adamu Muhammad Dokoro (Gombe)
Fotowa ta 004
Suna daga cikin siffofi mace saliha:
18, MAI YADDA DA HUKUNCIN ALLAH: Da kuma ikonsa kamar yadda Manzon Allah Yace" Mamaki ga al'amarin mutum musulmi,al'amarinsa duka alherine,in farin ciki yasameshi sai yagodewa Allah sai yazama alheri agareshi,in ciwo yasameshi sai yayi hakuri hakan yazama masa alheri"(Imam Muslim) Allah Yace "inacika ladan masu hakuri batare da hisabi ba" Suratul Zumar ayata 10.
19, MAI MAIDA AL'AMARI GA ALLAH: Mai bauta ma Allah tare da komawa ga Allah koda shaid'an ya shafeta idan ta tuna tana komawa ga Allah Mad'aukakin sarki.
20, MAI JIN CEWA ALLAH ZAI TAMBAYETA:Iyalenta domin tambayar da Allah zaiwa mace kan iyalen gida yafi na miji saboda tafi namijin sanin abunda ya bayyana fa halayyar yara acikin gida.Manzon Allah ( ) Yace Mace za'atambayeta gidan mijinta da 'ya'yanta kamar yadda yakamata
21, *ABIN DA YAFI DAMUNTA* :Shine yardan Allah,Tafi damuwa tasami yardan Allah kamar yadda Nana A'isha ta ruwaito hadisi daga Manzon Allah( ) Yana cewa Wanda yanemi yardan Allah ya isar masa daga mutane,wanda yanemi yardan mutane da fushin Allah,Allah zai barshi da mutane (Timidhi)
22, TANA MISALTUWA DA BAUTAWA ALLAH: Mai shiryarwace ga maganarta,da tafiyarta,da suturarta da aurenta,da bukukuwanta da sauran al'amarinta duka sai abinda addini yafad'i bata sa son zuciya tayi bid'a ko shishshigi.
23, TANA AIKI DOMIN TQIMAKON ADDININ ALLAH:Bata fifita duniya akan addini,kamar yadda Allah Yace Ban halici mutum da aljan ba sai don su bautamin (zariyat ayata 56)
24, MABUWAYYIYA DA KANTA:Da addininta ba kamar yadda wasu suke basu wulakanta kansu kuma su wulakanta addinincsu,mumini girma nasa ne kuma Allah ne Ya basu domin bai yarda da kaskancin ba wato shi addini.
25, BATA JINGINA KANTA GA KOWA SAI ALLAH: Wato Allah shine majibincin al'amarinta da Manzonsa,ma'ana shine mai bata umarni sai manzonsa,sai kuma umarnin da yadace dana Allah da manzonsa kamar yadda yagabata.
27, MAI UMURNI CE DA KYAWAWAN AYYUKA: Kuma mai hani ce da munanan ayyuka kamar yadda Alkah Yace Muminai maza da mata masoyan juna ne,kuma suna umurni da kyawawan ayyuka suna hana munanan ayyuka(Tauba aya71) .Kenan mai wa'azi ce kuma mai ilimi ba jahila ba zata yi wa'azi kuma tana taimakawa mata 'yan uwanta wajen ilimantarwa,wa'azi,nasiha da sauran ayyuka na gari.
Allah Yasa muna daga cikin wad'annan mata salihan.(Amin)
A sauraremu a fitowa na 5 in shaa Allah.
✍🏻 'Yar uwarku a musulunci:
Ummu Abdillah Gombe
Repost
September 2016
UMMAHATUL MUMININ
Comments
Post a Comment