Skip to main content

Makarantar rayuwa; kowa da ajinsa Daga: Sheikh Basheer Lawal Muhammad Zaria Hafizahullah


DAGA ZUCI ZUWA ZUCI

Makarantar rayuwa; kowa da ajinsa

Daga: Sheikh Basheer Lawal Muhammad Zaria Hafizahullah
13th Almuharram, 1441H
13th Satumba, 2019M

Ɗazu da safe Babban Malami Dr. Mansur Sokoto ya turo min wani rubutu cikin yaren Ingilishi mai taken: life is a class of one a ciki marubucin yana bada labarin wani biki da ya halarta na ƴar ɗaya daga cikin abokan karatunsa a jami'a, shekaru talatin da suka wuce, sai ya haɗu da wasu abokan karatun nasa, a nan ne ya ga yadda Allah mai iko ya banbanta rayuwarsu, a inda wasu sun fi wasu a wani fage, wasu kuma sun fi su a wani fagen, sai yake gane cewa: za ku iya yin makaranta ɗaya da mutum, kuma aji guda, amma a makarantar rayuwa ajinku ba guda ba
- Kana iya fin 'dan ajinku 'kwa'kwalwa shi kuma ya riga ka samun aiki.
- Kana iya rigarsa samun aiki ya riga ka aure.
- Yana iya rigarka samun aiki ka zo ka wuce shi a matsayi.
- Yana iya wuce ka a matsayi kai kuma ka fi shi shahara a duniya....
Wannan duk yana cikin tsarin Allah Buwayi Gagarerren Sarki.
Saboda haka:
- Ka zama mai yarda da ajin da Allah ya aje ka bayan ka yi abin da za ka iya yi na motsi, da kaiwa da komowa.
- Ka rik'a kallon ni'imomin da Allah yai maka, ta haka za ka iya gode masa.
- Ka rik'a dubi zuwa ga wad'anda ka wuce su ba wad'anda suka wuce ka ba.
- Ka fahimci ita rayuwa kamar zanen ziza take, lauye-lauye gare ta.
- Gane haka na saka ka zauna lafiya da Ubangijinka(Allah), da zuciyarka, da jikinka, da mutane gaba d'ayansu.
Allah ya saka ma wancan mai rubuta, da Dr Mansur mai turawa, da alkhairi.
Allah ya bamu ikon fahimtar irin wad'annan nau'ukan tsinkaye, da kuma aiki da su.
Na bar ku da wannan.

Comments

Popular posts from this blog

Addu'ar Neman Mijin/Matar Aure

TAMBAYA Assalamu Alaikum warahmatullah malam don Allah ina Neman fatawane Watace take Neman miji kasancewar duk masu  zuwa wurinta ba dagaske suke yi ba toh shi ne ta nemi taimako wurin malamin zaure yake bata rubutu tana sha daniyyar Allah ya sa ta dace. Toh malam abin tambaya anan shi ne shin menene makomar abin da ta aikata? shin malam tayi shirka ne ko kuwa tayi ba daidai ba? nagode. AMSA    Dafarko gameda shan rubutu muddin ayan QUR'ANI ne tsantsa babu wasu zane zanen hatimi, to ya halatta yadda IBN TAIMIYYA ya tabbatar a MAJMU'UL FATAWA, haka ma WAHEED ABDUSSALAM BAALY ya tabbar da hakan a SARIMUL BATTAR,    Amma in akasin haka ne haramun ne don yakan zama shirka ne da surkulle,    Fadin cewa Malamin zaure ne na gargajiya to galibi irin na shirkan sukeyi, don haka ki tuba tsakanin ki da ALLAH da alkawarin bazaki sake zuwa wurin su ba don kare addinin ki da mutuncin ki,    Don samun biyan bukatun ki sai kizage da addu'a da kiyamul...

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI Fitowa na 3

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI               NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 3 (kuma fitowa ta karshe): HAKKOKIN MACE A KAN MIJINTA: Kamar yadda miji yake da hakkoki akan matarsa, haka ita ma matar take da hakkokin akan mijinta, daga cikin wadannan hakkoki akwai : 1 - SADAKI: Hakkin mace ne a bata sadakinta, yayin da za a aure ta, Allah Madaukakin Sarki ya ce: “Ku bawa mata sadakinsu kyauta” (Nisa’i 4). A wani wurin Allah Madaukakin Sarki cewa ya yi:   “Ku aure su da izinin iyalansu, ku basu sadakinsu da adalci” (Addalak : 25). 2 – CIYARWA: Hakkin mata ne akan mijinta ya ciyar da ita, gwargwadon halinsa, koda kuwa tana da wadata da arziki, Allah Madaukakin Sarki yana cewa :  “Mai wadata ya ciyar daga wadatarsa, wanda kuwa aka kuntatawa arzikinsa, to ya ciyar daga abin da Allah ya bashi, Allah baya dorawa wata rai sai abin da ya bata” (Dalaq : 7). An tambayi Manzon Allah, tsira da amincin ...

Hakkokin Ma'aurata a Shari'ar Musulunci Fitowa na 2

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI       NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 2 3 -  YIN ADO DA KWALLIYA: Hakkin miji ne akan matarsa ta yi masa ado da kwalliya, don ta kare shi daga kallon wasu matan daban, wadanda shari’a ta hana shi kallonsu. Mata sun kasance suna kwalliya da dan kunne da awarwaro da munduwa tun a zamanin Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kamar yadda hadisin Abdullahi dan Abbas, Allah Ya kara yarda a gare shi a cikin Sahihul Bukhari da Muslim ya nuna, a lokacin da Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya je wajensu, ya yi musu wa’azi a ranar idi. Kuma saboda Mahimmanci mace ta yi wa mijinta kwalliya, ta zama a shiga mai kyau mai jan hankali, Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya hana miji ya dawo wa iyalinsa daga tafiya cikin dare, ya shigo gida ba tare da sun san da zuwansa ba, An karbo daga Jabir, Allah Ya kara yarda a gare shi, ya ce, Manz...