Skip to main content

WASU ABUBUAWAN DA SUKE YAYE BALA'I, DAMUWA DA DUK WANI Tsanani DA MUTUM YA TSINCI KANSA A CIKI



WASU ABUBUAWAN DA SUKE YAYE BALA'I, DAMUWA DA DUK WANI Tsanani DA MUTUM YA TSINCI KANSA A CIKI......

Daga
Sheikh Dr. Sani Umar R/Lemo

1. Kyautata imani da Allah da nisantar abin da yake tauye imani: Allah ya yi alkawarin taimakon bayinsa muminai, da ba su nasara akan abokan gabarsu. Don haka matukar akwai imani da Allah a zukatan bayi to Allah ba zai tozarta su ba.

2. Tuba da Istigfari da komawa zuwa ga Allah.

3. Yawaita ayyuka na kwarai, saboda ayyukan kwarai sukan kawo wa zuciya nutsuwa, kamar yadda munanan ayyuka sukan kawo wa zuciya bakin ciki da damuwa da kunci.

4. Yawaita Sadaka: musammam ma a boye ba tare da an sani ba, ya tabbata a hadisi Manzon Allah S.A.W ya ce “Aikata kyawawan ayyuka suna kawar da munanan abubuwa, sadakar boye tana kawar da fushin Ubangiji, sada zumunci yana kara tsawon rayuwa, dukkan aikin alheri sadaka ne, masu aikin alheri a duniya, su ne ma’abota alheri a lahira, masu munanan ayyuka a duniya, su ne masu ma’abota mummuna a lahira, farkon wadanda za su shiga Aljannah su ne masu aikata kyawawan ayyuka”.Dabaran i ne ya rawaito shi. .

5. Addu’a: ba don addu’a ba da mutane da yawa sun halaka. Allah madaukakin Sarki yana jarrabar bayinsa da bala’i don su koma gare shi, su kaskantar da kai da addu’a, idan suka koma zuwa gare shi, suka kasakantar da kai sai ya yaye musu. .

6. Umarni da kyakkyawan aiki da hana mummuna: Allah ba zai halaka al’umma ba, matukar akwai masu umarni da kyakkyawan aiki da hana mummuna. .

7. Nisantar Zalunci : Allah ya halakar da al’ummu da yawa saboda zalunci. Mafi girman zalunci shi ne shirka da kafirci, sai zaluntar bayin Allah a cikin dukiyarsu da mutuncinsu da jininsu, mu nisanci zalunci mu zauna lafiya. .

8. Zikiri wato ambaton Allah, da baki da zuciya da gabbai. Da ambaton Allah ne zukata suke nutsuwa.

Allah ya yafe mana kurakuranmu. Allah ka amshi tubanmu. Amin.



Comments

Popular posts from this blog

Addu'ar Neman Mijin/Matar Aure

TAMBAYA Assalamu Alaikum warahmatullah malam don Allah ina Neman fatawane Watace take Neman miji kasancewar duk masu  zuwa wurinta ba dagaske suke yi ba toh shi ne ta nemi taimako wurin malamin zaure yake bata rubutu tana sha daniyyar Allah ya sa ta dace. Toh malam abin tambaya anan shi ne shin menene makomar abin da ta aikata? shin malam tayi shirka ne ko kuwa tayi ba daidai ba? nagode. AMSA    Dafarko gameda shan rubutu muddin ayan QUR'ANI ne tsantsa babu wasu zane zanen hatimi, to ya halatta yadda IBN TAIMIYYA ya tabbatar a MAJMU'UL FATAWA, haka ma WAHEED ABDUSSALAM BAALY ya tabbar da hakan a SARIMUL BATTAR,    Amma in akasin haka ne haramun ne don yakan zama shirka ne da surkulle,    Fadin cewa Malamin zaure ne na gargajiya to galibi irin na shirkan sukeyi, don haka ki tuba tsakanin ki da ALLAH da alkawarin bazaki sake zuwa wurin su ba don kare addinin ki da mutuncin ki,    Don samun biyan bukatun ki sai kizage da addu'a da kiyamul...

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI Fitowa na 3

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI               NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 3 (kuma fitowa ta karshe): HAKKOKIN MACE A KAN MIJINTA: Kamar yadda miji yake da hakkoki akan matarsa, haka ita ma matar take da hakkokin akan mijinta, daga cikin wadannan hakkoki akwai : 1 - SADAKI: Hakkin mace ne a bata sadakinta, yayin da za a aure ta, Allah Madaukakin Sarki ya ce: “Ku bawa mata sadakinsu kyauta” (Nisa’i 4). A wani wurin Allah Madaukakin Sarki cewa ya yi:   “Ku aure su da izinin iyalansu, ku basu sadakinsu da adalci” (Addalak : 25). 2 – CIYARWA: Hakkin mata ne akan mijinta ya ciyar da ita, gwargwadon halinsa, koda kuwa tana da wadata da arziki, Allah Madaukakin Sarki yana cewa :  “Mai wadata ya ciyar daga wadatarsa, wanda kuwa aka kuntatawa arzikinsa, to ya ciyar daga abin da Allah ya bashi, Allah baya dorawa wata rai sai abin da ya bata” (Dalaq : 7). An tambayi Manzon Allah, tsira da amincin ...

Hakkokin Ma'aurata a Shari'ar Musulunci Fitowa na 2

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI       NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 2 3 -  YIN ADO DA KWALLIYA: Hakkin miji ne akan matarsa ta yi masa ado da kwalliya, don ta kare shi daga kallon wasu matan daban, wadanda shari’a ta hana shi kallonsu. Mata sun kasance suna kwalliya da dan kunne da awarwaro da munduwa tun a zamanin Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kamar yadda hadisin Abdullahi dan Abbas, Allah Ya kara yarda a gare shi a cikin Sahihul Bukhari da Muslim ya nuna, a lokacin da Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya je wajensu, ya yi musu wa’azi a ranar idi. Kuma saboda Mahimmanci mace ta yi wa mijinta kwalliya, ta zama a shiga mai kyau mai jan hankali, Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya hana miji ya dawo wa iyalinsa daga tafiya cikin dare, ya shigo gida ba tare da sun san da zuwansa ba, An karbo daga Jabir, Allah Ya kara yarda a gare shi, ya ce, Manz...