Skip to main content

BABU HADISI INGANTACCE AKAN YAWAN KWANAKIN HAILA ! !

Tambaya


Assalamu alaikum 

Na karanta amsar da malam ya bada wadda ban fahimce taba, Abusa tambayar da akayi mashi. Ta zuwan jini duk sati tare da cewa taje asibiti Amman sunce saidai tayi hakuri in na fahimci tambayar .

Hukncin matar da take da irin wannan lalora shine : Zata bar salla a duk lokacin da jini yazo mata in lokacin yin al'adattane ko da ya doge harfiye da kwanakin da takeyi mutukar bewoce kwana(15) ba, Amman in ya woce haka zatayi wanka tayi salla don haila ba ta wuce kwana(15).


Amsa


Wa'alaykumussalam 

Abin da abokina ya fada shi ne fatawar Malikiyya da Shafi'iyya, saidai babu ko hadisi daya da ya tabbata akan cewa : jinin haila ba ya wuce kwana sha biyar, duk hadisan da suka zo akan haka ba su inganta ba, daga ciki akwai hadisin da aka rawaito cewa: "An tambayi Annabi s.a.w game da tawayar addinin mace, sai ya ce: "Daya daga cikinsu zata zauna rabin rayuwarta ba ta sallah"

Ibnul Jauzu ya raunana shi a littafinsa Attahkik 1\263 haka Annawawy shi ma ya ce: hadisin karya ne, kamar yadda ya zo a AlMajmu''u 2\405, 

Ibnu Abdulhady shi ma ya raunana shi a cikin Tankihu attahkiki1\414, Baihaki a cikin Ma'arifatu assunan wal-athar,2\145 yana cewa: Na nemi hadisin da sanadi a littattafan hadisi amma ban taba ganinsa ba, 

Haka nan Hanafiyya sun tafi akan cewa : Jinin haila ba ya wuce kwana goma, saidai duk hadisan da suka kafa hujja da su babu ingantacce a ciki, Duba Al-ilal Al-mutanahiyah na Ibnu Al-jauzy 2\382.

Zance mafi inganci shi ne haila ba ta da wasu kwanaki na musamman, kamar yadda sheik Ibnu Uthaimin ya tabbatar da haka a littafinsa na Dima'uddabi'iyya, tun da Allah da manzonsa sun rataya hukunce-hukuncenta ne da samuwarta, don haka duk inda aka samu jinin haila da sifofinsa (baki, karni) hukuncinta yana tabbata, saidai idan ya kasance mafi yawan rayuwa ko dukkanta, a lokacin ne zai zama jinin cuta. 


 Allah ne mafi sani


Dr. Jamilu Zarewa


Daga ZAUREN FIQHUS SUNNAH

Comments

Popular posts from this blog

Addu'ar Neman Mijin/Matar Aure

TAMBAYA Assalamu Alaikum warahmatullah malam don Allah ina Neman fatawane Watace take Neman miji kasancewar duk masu  zuwa wurinta ba dagaske suke yi ba toh shi ne ta nemi taimako wurin malamin zaure yake bata rubutu tana sha daniyyar Allah ya sa ta dace. Toh malam abin tambaya anan shi ne shin menene makomar abin da ta aikata? shin malam tayi shirka ne ko kuwa tayi ba daidai ba? nagode. AMSA    Dafarko gameda shan rubutu muddin ayan QUR'ANI ne tsantsa babu wasu zane zanen hatimi, to ya halatta yadda IBN TAIMIYYA ya tabbatar a MAJMU'UL FATAWA, haka ma WAHEED ABDUSSALAM BAALY ya tabbar da hakan a SARIMUL BATTAR,    Amma in akasin haka ne haramun ne don yakan zama shirka ne da surkulle,    Fadin cewa Malamin zaure ne na gargajiya to galibi irin na shirkan sukeyi, don haka ki tuba tsakanin ki da ALLAH da alkawarin bazaki sake zuwa wurin su ba don kare addinin ki da mutuncin ki,    Don samun biyan bukatun ki sai kizage da addu'a da kiyamul...

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI Fitowa na 3

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI               NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 3 (kuma fitowa ta karshe): HAKKOKIN MACE A KAN MIJINTA: Kamar yadda miji yake da hakkoki akan matarsa, haka ita ma matar take da hakkokin akan mijinta, daga cikin wadannan hakkoki akwai : 1 - SADAKI: Hakkin mace ne a bata sadakinta, yayin da za a aure ta, Allah Madaukakin Sarki ya ce: “Ku bawa mata sadakinsu kyauta” (Nisa’i 4). A wani wurin Allah Madaukakin Sarki cewa ya yi:   “Ku aure su da izinin iyalansu, ku basu sadakinsu da adalci” (Addalak : 25). 2 – CIYARWA: Hakkin mata ne akan mijinta ya ciyar da ita, gwargwadon halinsa, koda kuwa tana da wadata da arziki, Allah Madaukakin Sarki yana cewa :  “Mai wadata ya ciyar daga wadatarsa, wanda kuwa aka kuntatawa arzikinsa, to ya ciyar daga abin da Allah ya bashi, Allah baya dorawa wata rai sai abin da ya bata” (Dalaq : 7). An tambayi Manzon Allah, tsira da amincin ...

Hakkokin Ma'aurata a Shari'ar Musulunci Fitowa na 2

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI       NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 2 3 -  YIN ADO DA KWALLIYA: Hakkin miji ne akan matarsa ta yi masa ado da kwalliya, don ta kare shi daga kallon wasu matan daban, wadanda shari’a ta hana shi kallonsu. Mata sun kasance suna kwalliya da dan kunne da awarwaro da munduwa tun a zamanin Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kamar yadda hadisin Abdullahi dan Abbas, Allah Ya kara yarda a gare shi a cikin Sahihul Bukhari da Muslim ya nuna, a lokacin da Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya je wajensu, ya yi musu wa’azi a ranar idi. Kuma saboda Mahimmanci mace ta yi wa mijinta kwalliya, ta zama a shiga mai kyau mai jan hankali, Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya hana miji ya dawo wa iyalinsa daga tafiya cikin dare, ya shigo gida ba tare da sun san da zuwansa ba, An karbo daga Jabir, Allah Ya kara yarda a gare shi, ya ce, Manz...