Skip to main content

MATANA TA HAIHU A RAMADAN KUMA GA WATA RAMADAN DIN TA ZAGAYO TANA DAUKE DA WANI CIKIN

Tambaya

Assalamualaikum, tambaya ta, matanane ta haifu lokacin azumi, kamin azumi ya zagayo kuma ta dau Wani ciki bata Samu ta biya Wanda ta sha ba, domin kuwa tana shayarwa kuma ga ciki, ta fara ramawa a wannan halin, ranar farko tana shan Ruwa Sai asibiti dama tana da ulser amma ba Wanda zai Hana azumi ba, ganin haka nikuma Na tsorata Sai Na hanata azumin. Mallam tambaya Na shine 1.inada laifi ne Na hanata azumi 2. Zata Rama azuminne koko shayarwa koko dukka biyu 3. In shayarwa ne zata iya Bawa mutum daya dukkan mudunabi a lokaci daya koko Ko Wani rana za a Bawa mutum daya.

Amsa

Wa'alaykumussalam

1. Ba kada laifi domin shari'a tayi rangwame ga wanda ba yada lafiya da ya aje azumi sai ya rama a wasu lokuttan na daban bayan ya samu sauki, kamar yadda yazo cikin fadar Allah cikin suratul bakara 184.

2. Idan har zata iya ramawa to ta rama duk abinda ta sha, idan kuma bazata iya ramawa ba bisa bincike na likitoci masana addini toh zata ciyar ne kawai babu ramako akan ta, malamai na hujja da fadar Allah suratul bakara 184.

3. Zata ciyar da miskini daya kowane yini, idan kuma ta hada na adadin da ake binta ta baiwa miskini daya duka shima babu laifi, kamar yadda Sheihul islam ibn taymiyya ya bada fatawa cikin littafin sa majmoo'ul fatawa 15/203. 

Wallahu A'alam

Malam Nuruddeen Muhammad Mujaheed

Daga ZAUREN FIQHUS SUNNAH

Comments

Popular posts from this blog

Addu'ar Neman Mijin/Matar Aure

TAMBAYA Assalamu Alaikum warahmatullah malam don Allah ina Neman fatawane Watace take Neman miji kasancewar duk masu  zuwa wurinta ba dagaske suke yi ba toh shi ne ta nemi taimako wurin malamin zaure yake bata rubutu tana sha daniyyar Allah ya sa ta dace. Toh malam abin tambaya anan shi ne shin menene makomar abin da ta aikata? shin malam tayi shirka ne ko kuwa tayi ba daidai ba? nagode. AMSA    Dafarko gameda shan rubutu muddin ayan QUR'ANI ne tsantsa babu wasu zane zanen hatimi, to ya halatta yadda IBN TAIMIYYA ya tabbatar a MAJMU'UL FATAWA, haka ma WAHEED ABDUSSALAM BAALY ya tabbar da hakan a SARIMUL BATTAR,    Amma in akasin haka ne haramun ne don yakan zama shirka ne da surkulle,    Fadin cewa Malamin zaure ne na gargajiya to galibi irin na shirkan sukeyi, don haka ki tuba tsakanin ki da ALLAH da alkawarin bazaki sake zuwa wurin su ba don kare addinin ki da mutuncin ki,    Don samun biyan bukatun ki sai kizage da addu'a da kiyamul...

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI Fitowa na 3

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI               NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 3 (kuma fitowa ta karshe): HAKKOKIN MACE A KAN MIJINTA: Kamar yadda miji yake da hakkoki akan matarsa, haka ita ma matar take da hakkokin akan mijinta, daga cikin wadannan hakkoki akwai : 1 - SADAKI: Hakkin mace ne a bata sadakinta, yayin da za a aure ta, Allah Madaukakin Sarki ya ce: “Ku bawa mata sadakinsu kyauta” (Nisa’i 4). A wani wurin Allah Madaukakin Sarki cewa ya yi:   “Ku aure su da izinin iyalansu, ku basu sadakinsu da adalci” (Addalak : 25). 2 – CIYARWA: Hakkin mata ne akan mijinta ya ciyar da ita, gwargwadon halinsa, koda kuwa tana da wadata da arziki, Allah Madaukakin Sarki yana cewa :  “Mai wadata ya ciyar daga wadatarsa, wanda kuwa aka kuntatawa arzikinsa, to ya ciyar daga abin da Allah ya bashi, Allah baya dorawa wata rai sai abin da ya bata” (Dalaq : 7). An tambayi Manzon Allah, tsira da amincin ...

Hakkokin Ma'aurata a Shari'ar Musulunci Fitowa na 2

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI       NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 2 3 -  YIN ADO DA KWALLIYA: Hakkin miji ne akan matarsa ta yi masa ado da kwalliya, don ta kare shi daga kallon wasu matan daban, wadanda shari’a ta hana shi kallonsu. Mata sun kasance suna kwalliya da dan kunne da awarwaro da munduwa tun a zamanin Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kamar yadda hadisin Abdullahi dan Abbas, Allah Ya kara yarda a gare shi a cikin Sahihul Bukhari da Muslim ya nuna, a lokacin da Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya je wajensu, ya yi musu wa’azi a ranar idi. Kuma saboda Mahimmanci mace ta yi wa mijinta kwalliya, ta zama a shiga mai kyau mai jan hankali, Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya hana miji ya dawo wa iyalinsa daga tafiya cikin dare, ya shigo gida ba tare da sun san da zuwansa ba, An karbo daga Jabir, Allah Ya kara yarda a gare shi, ya ce, Manz...