Skip to main content

TUBAN WANI MAKWABCIN IMAMU AHMAD BN HANBAL, RAHIMAHULLAH

A samu daga Ja'afar al-Saa'ig, ya ce: 


Akwai wani mutum makwabcin Imam Ahmad wanda yake mai yawan sabon Allah, sai ga shi wata rana ya zo wajen Imamu Ahmad, Allah Ta'ala Ya yi masa rahama, ya yi masa sallama, sai Imamu Ahmad bai amsa masa sosai ba, sannan bai mika masa hannu ba. 


Sai mutumin ya ce: Yaa Baban Abdullahi, me ya sa baka bani hannu mun gaisa ba? Alhalin na daina aikata abin da kake tsamanina da shi, saboda wani mafarki da na yi. 


Sai Imamu Ahmad, Allah Ta'ala Ya yi masa rahama, ya ce: me ka gani a mafarkin? 


Ya ce: Na ga Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, a saman kasa sannan ga mutane masu yawa suna zaune a karkashin shi. Sai wadannan mutanen suna taso daya bayan daya suna zuwa wajen Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, su na cewa ka yi mana addu'a, sai Manzon Allah, Ya yi musu addu'a, har sai da suka kare saura ni kadai. 


Ya ce sai na yi nufin in mike ni ma in je in ce ya yi mun addu'a, amma sai na ji kunya ta kama ni saboda irin zunubai da nake aikatawa. 


Sai Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya kira ni Ya ce mun: Me ya sa baka taso ka ce in yi maka addu'a ba? 


Sai na ce: Babu abin da ya hana ni face kunya na munin abun da nake aikatawa . 


Sai ya ce mun: Idan har kunya ce ta hana ka to taso ka zo kai ma ka ce in roka maka Allah DOMIN BAKA ZAGIN KOWA DAYA DAGA CIKIN SAHABBAINA. 


Ya ce: sai na mike na je Ya roka mun Allah. 


Bayan na farka daga bacci sai na ji ina kyamatar dukkan zunuban da na kasance ina aikatawa. 


Sai Imam Ahmad, Allah Ta'ala Ya yi masa rahama ya ce: Yaa Ja'afar, Yaa kai wannan mutum ku bayar da wannan labari kuma ku kiyaye wannan labarin domin zai amfanar. 


Ga mai son duba wannan labari zai iya karanta littafin قصص التائبين na babban Malami محمود المصري أبو عمار shafin na 228 ko a duba littafin كتاب التوابين shafi na 178.


Yaa Allah ka tsare mu daga aikata zunubai kuma Ka tsare mu daga ZAGIN SAHABBAN MANZON ALLAH. 


Dan uwanku a Musulunci:

Umar Shehu Zaria.

07/03/2017

Comments

Popular posts from this blog

Addu'ar Neman Mijin/Matar Aure

TAMBAYA Assalamu Alaikum warahmatullah malam don Allah ina Neman fatawane Watace take Neman miji kasancewar duk masu  zuwa wurinta ba dagaske suke yi ba toh shi ne ta nemi taimako wurin malamin zaure yake bata rubutu tana sha daniyyar Allah ya sa ta dace. Toh malam abin tambaya anan shi ne shin menene makomar abin da ta aikata? shin malam tayi shirka ne ko kuwa tayi ba daidai ba? nagode. AMSA    Dafarko gameda shan rubutu muddin ayan QUR'ANI ne tsantsa babu wasu zane zanen hatimi, to ya halatta yadda IBN TAIMIYYA ya tabbatar a MAJMU'UL FATAWA, haka ma WAHEED ABDUSSALAM BAALY ya tabbar da hakan a SARIMUL BATTAR,    Amma in akasin haka ne haramun ne don yakan zama shirka ne da surkulle,    Fadin cewa Malamin zaure ne na gargajiya to galibi irin na shirkan sukeyi, don haka ki tuba tsakanin ki da ALLAH da alkawarin bazaki sake zuwa wurin su ba don kare addinin ki da mutuncin ki,    Don samun biyan bukatun ki sai kizage da addu'a da kiyamul...

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI Fitowa na 3

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI               NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 3 (kuma fitowa ta karshe): HAKKOKIN MACE A KAN MIJINTA: Kamar yadda miji yake da hakkoki akan matarsa, haka ita ma matar take da hakkokin akan mijinta, daga cikin wadannan hakkoki akwai : 1 - SADAKI: Hakkin mace ne a bata sadakinta, yayin da za a aure ta, Allah Madaukakin Sarki ya ce: “Ku bawa mata sadakinsu kyauta” (Nisa’i 4). A wani wurin Allah Madaukakin Sarki cewa ya yi:   “Ku aure su da izinin iyalansu, ku basu sadakinsu da adalci” (Addalak : 25). 2 – CIYARWA: Hakkin mata ne akan mijinta ya ciyar da ita, gwargwadon halinsa, koda kuwa tana da wadata da arziki, Allah Madaukakin Sarki yana cewa :  “Mai wadata ya ciyar daga wadatarsa, wanda kuwa aka kuntatawa arzikinsa, to ya ciyar daga abin da Allah ya bashi, Allah baya dorawa wata rai sai abin da ya bata” (Dalaq : 7). An tambayi Manzon Allah, tsira da amincin ...

Hakkokin Ma'aurata a Shari'ar Musulunci Fitowa na 2

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI       NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 2 3 -  YIN ADO DA KWALLIYA: Hakkin miji ne akan matarsa ta yi masa ado da kwalliya, don ta kare shi daga kallon wasu matan daban, wadanda shari’a ta hana shi kallonsu. Mata sun kasance suna kwalliya da dan kunne da awarwaro da munduwa tun a zamanin Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kamar yadda hadisin Abdullahi dan Abbas, Allah Ya kara yarda a gare shi a cikin Sahihul Bukhari da Muslim ya nuna, a lokacin da Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya je wajensu, ya yi musu wa’azi a ranar idi. Kuma saboda Mahimmanci mace ta yi wa mijinta kwalliya, ta zama a shiga mai kyau mai jan hankali, Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya hana miji ya dawo wa iyalinsa daga tafiya cikin dare, ya shigo gida ba tare da sun san da zuwansa ba, An karbo daga Jabir, Allah Ya kara yarda a gare shi, ya ce, Manz...