Skip to main content

AKWAI ZAKKA A CIKIN HAJAR KASUWANCI !

Tambaya

Assalamu alaikum. Malam, Na karbi loan a Ja'iz Bank shekaru uku da suka wuce, na kuma shiga harkar gina gidaje, a yanzu na gama biyan kudin a wannan January 2020.
Gidajen da na gina a Millinion City 2 & 3 bedroom flats ne, amma fa suna kasuwa.

1.Tambaya ta ita ce, shin akwai Zakkah a cikin wannan, idan akwai, yaushe ya kamata a fitar?
Saboda a yanzu shekara daya kenan gidajen na kasuwa ba'a riga an sayar ba.
2. Tambaya ta biyu.
Mai dakina tana sana'ar kayan Kitchen yau shekara Ukku, Kuma Allah yasa Albarka a cikin sana'ar, yaushe ya kamata ta fidda Zakkah? saboda, wasu kudin suna hannun mutane a matsayin bashi, wasu hajane watau (kayan kitchen) ba'a riga an sayar ba.
Sannan akwai kudi a banki, amma basu isa Zakkah ba. 
Shin Yaya za'a fitar da Zakkah a wannan halin? saboda idan aka hada kudin dake banki, da hajar dake kasa da kudaden dake hannun mutane na bashi, kudin sun kai Nisabin Zakkah.

Na gode, Allah Ya saka da Alheri, amin.

Amsa
Wa alaikum assalam
Gidajan da aka yi don siye da siyarwa ana fitar musu da Zakka in sun Shekara kuma sun kai nisabi, saboda sun zama kayan Kasuwanci, kayan Kasuwanci kuma ana fitar musu da Zakka kamar yadda Ibnu Abi-zaid Alkairawany ya yi bayani a Risala shafi na (66).

Mutumin da yake Kasuwanci, ya wajaba duk Shekara ya kaddara hajarsa da kuma kudin da suke hannunsa da kuma na banki, mutukar jumalarsu sun kai Nisabi kuma sun Shekara, zai fitar da Zakka.
Ana kasa jumlarsu ne gida Arba'in, sai a bada kashi guda.

Allah ne Mafi sani

Dr. Jamilu Yusuf Zarewa


Daga ZAUREN FIQHUS SUNNAH

Comments

Popular posts from this blog

Addu'ar Neman Mijin/Matar Aure

TAMBAYA Assalamu Alaikum warahmatullah malam don Allah ina Neman fatawane Watace take Neman miji kasancewar duk masu  zuwa wurinta ba dagaske suke yi ba toh shi ne ta nemi taimako wurin malamin zaure yake bata rubutu tana sha daniyyar Allah ya sa ta dace. Toh malam abin tambaya anan shi ne shin menene makomar abin da ta aikata? shin malam tayi shirka ne ko kuwa tayi ba daidai ba? nagode. AMSA    Dafarko gameda shan rubutu muddin ayan QUR'ANI ne tsantsa babu wasu zane zanen hatimi, to ya halatta yadda IBN TAIMIYYA ya tabbatar a MAJMU'UL FATAWA, haka ma WAHEED ABDUSSALAM BAALY ya tabbar da hakan a SARIMUL BATTAR,    Amma in akasin haka ne haramun ne don yakan zama shirka ne da surkulle,    Fadin cewa Malamin zaure ne na gargajiya to galibi irin na shirkan sukeyi, don haka ki tuba tsakanin ki da ALLAH da alkawarin bazaki sake zuwa wurin su ba don kare addinin ki da mutuncin ki,    Don samun biyan bukatun ki sai kizage da addu'a da kiyamul...

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI Fitowa na 3

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI               NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 3 (kuma fitowa ta karshe): HAKKOKIN MACE A KAN MIJINTA: Kamar yadda miji yake da hakkoki akan matarsa, haka ita ma matar take da hakkokin akan mijinta, daga cikin wadannan hakkoki akwai : 1 - SADAKI: Hakkin mace ne a bata sadakinta, yayin da za a aure ta, Allah Madaukakin Sarki ya ce: “Ku bawa mata sadakinsu kyauta” (Nisa’i 4). A wani wurin Allah Madaukakin Sarki cewa ya yi:   “Ku aure su da izinin iyalansu, ku basu sadakinsu da adalci” (Addalak : 25). 2 – CIYARWA: Hakkin mata ne akan mijinta ya ciyar da ita, gwargwadon halinsa, koda kuwa tana da wadata da arziki, Allah Madaukakin Sarki yana cewa :  “Mai wadata ya ciyar daga wadatarsa, wanda kuwa aka kuntatawa arzikinsa, to ya ciyar daga abin da Allah ya bashi, Allah baya dorawa wata rai sai abin da ya bata” (Dalaq : 7). An tambayi Manzon Allah, tsira da amincin ...

Hakkokin Ma'aurata a Shari'ar Musulunci Fitowa na 2

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI       NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 2 3 -  YIN ADO DA KWALLIYA: Hakkin miji ne akan matarsa ta yi masa ado da kwalliya, don ta kare shi daga kallon wasu matan daban, wadanda shari’a ta hana shi kallonsu. Mata sun kasance suna kwalliya da dan kunne da awarwaro da munduwa tun a zamanin Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kamar yadda hadisin Abdullahi dan Abbas, Allah Ya kara yarda a gare shi a cikin Sahihul Bukhari da Muslim ya nuna, a lokacin da Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya je wajensu, ya yi musu wa’azi a ranar idi. Kuma saboda Mahimmanci mace ta yi wa mijinta kwalliya, ta zama a shiga mai kyau mai jan hankali, Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya hana miji ya dawo wa iyalinsa daga tafiya cikin dare, ya shigo gida ba tare da sun san da zuwansa ba, An karbo daga Jabir, Allah Ya kara yarda a gare shi, ya ce, Manz...