Skip to main content

WANDA BAI SAMU DAMAR YIN JUMA'A BA, ZAI IYA SALLAR AZAHAR A JAM'I !

Tambaya
Assalamu alaikum, don Allah a taimaka Mana da fatawa, a Jihar mu ta Nasarawa an fitar da umarnin hana sallar Jumu'a, shin
za mu iya kiran Sallah muyi Azahar a masallatan unguwar mu ?

Amsa

Wa alaikum assalam
Garuruwan da aka hana sallar Juma'a, aka yarda su yi Salloli guda biyar a cikin Jam'i, saboda hana yaduwar cutar Corona, ya halatta su yi Sallar Azahar a madadinta a cikin Jam'i a masallatansu su kira Sallah, su tada Ikama, saboda Malamai da yawa suna cewa duk wanda ya rasa Sallar Juma'a saboda wani uzuri karbabbe ko wanda yake yawan aukuwa ya halatta ya yi Azahar a cikin Jam'i a Masallacin da aka yi Juma'ar, tare da Kiran Sallah da Ikama, mutukar ba'a ji tsoran fitina ba ko kuma tunanin rashin cancantar limamin da ya jagoranci Sallar, Kamar yadda ya halatta ya yi a gida tare da iyalansa.

Don neman karin bayani duba: Almugny 2/99 da kuma Hilyatul-ulama'i Fi Ma'arifati mazahibil Fukaha'i na Kaffal 2/226.

Ya wajaba mu yawaita neman gafara a wajan Allah, saboda wasu lokutan idan zunubai suka yi yawa, Allah yana iya dakile bawansa daga aikin da zai kusantar da shi izuwa gare shi, Kamar yadda Allah ya yi bayani a suratu Attaubah aya (46).

Allah ne mafi sani.

Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

Comments

Popular posts from this blog

Addu'ar Neman Mijin/Matar Aure

TAMBAYA Assalamu Alaikum warahmatullah malam don Allah ina Neman fatawane Watace take Neman miji kasancewar duk masu  zuwa wurinta ba dagaske suke yi ba toh shi ne ta nemi taimako wurin malamin zaure yake bata rubutu tana sha daniyyar Allah ya sa ta dace. Toh malam abin tambaya anan shi ne shin menene makomar abin da ta aikata? shin malam tayi shirka ne ko kuwa tayi ba daidai ba? nagode. AMSA    Dafarko gameda shan rubutu muddin ayan QUR'ANI ne tsantsa babu wasu zane zanen hatimi, to ya halatta yadda IBN TAIMIYYA ya tabbatar a MAJMU'UL FATAWA, haka ma WAHEED ABDUSSALAM BAALY ya tabbar da hakan a SARIMUL BATTAR,    Amma in akasin haka ne haramun ne don yakan zama shirka ne da surkulle,    Fadin cewa Malamin zaure ne na gargajiya to galibi irin na shirkan sukeyi, don haka ki tuba tsakanin ki da ALLAH da alkawarin bazaki sake zuwa wurin su ba don kare addinin ki da mutuncin ki,    Don samun biyan bukatun ki sai kizage da addu'a da kiyamul...

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI Fitowa na 3

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI               NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 3 (kuma fitowa ta karshe): HAKKOKIN MACE A KAN MIJINTA: Kamar yadda miji yake da hakkoki akan matarsa, haka ita ma matar take da hakkokin akan mijinta, daga cikin wadannan hakkoki akwai : 1 - SADAKI: Hakkin mace ne a bata sadakinta, yayin da za a aure ta, Allah Madaukakin Sarki ya ce: “Ku bawa mata sadakinsu kyauta” (Nisa’i 4). A wani wurin Allah Madaukakin Sarki cewa ya yi:   “Ku aure su da izinin iyalansu, ku basu sadakinsu da adalci” (Addalak : 25). 2 – CIYARWA: Hakkin mata ne akan mijinta ya ciyar da ita, gwargwadon halinsa, koda kuwa tana da wadata da arziki, Allah Madaukakin Sarki yana cewa :  “Mai wadata ya ciyar daga wadatarsa, wanda kuwa aka kuntatawa arzikinsa, to ya ciyar daga abin da Allah ya bashi, Allah baya dorawa wata rai sai abin da ya bata” (Dalaq : 7). An tambayi Manzon Allah, tsira da amincin ...

Hakkokin Ma'aurata a Shari'ar Musulunci Fitowa na 2

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI       NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 2 3 -  YIN ADO DA KWALLIYA: Hakkin miji ne akan matarsa ta yi masa ado da kwalliya, don ta kare shi daga kallon wasu matan daban, wadanda shari’a ta hana shi kallonsu. Mata sun kasance suna kwalliya da dan kunne da awarwaro da munduwa tun a zamanin Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kamar yadda hadisin Abdullahi dan Abbas, Allah Ya kara yarda a gare shi a cikin Sahihul Bukhari da Muslim ya nuna, a lokacin da Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya je wajensu, ya yi musu wa’azi a ranar idi. Kuma saboda Mahimmanci mace ta yi wa mijinta kwalliya, ta zama a shiga mai kyau mai jan hankali, Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya hana miji ya dawo wa iyalinsa daga tafiya cikin dare, ya shigo gida ba tare da sun san da zuwansa ba, An karbo daga Jabir, Allah Ya kara yarda a gare shi, ya ce, Manz...