Skip to main content

SUNNONI DA LADUBBAN RANAR IDI

SUNNONI DA LADUBBAN RANAR IDI

1️⃣ YIN WANKA KAFIN FITA SALLAH

Ya inganta a cikin Muwaɗɗa na Imamu Malik, Rahimahullah, 428, cewa: Abdullahi Ɗan Umar, Radhiyallahu anhu, ya kasance yana yin wanka kafin ya fita sallar idi. 

2️⃣ CIN ABINCI KAFIN FITA IDI IDAN KARAMAR SALLAH CE DA KUMA CIN ABINCI BAYAN IDI IDAN IDIN LAYYA NE:

Hadisi ya inganta daga Anas Ɗan Malik cewa: Manzon Allah, sallallahu alaihi wa sallama, ya kasance ba ya fita sallar idi na karamar Sallah har sai ya ci dabino kuma ya kan ci mara ne ( wato 1 ko 3 ko 5 ko 7...). Bukhari ya riwaito 953.

Duk wanda bai samu dabino ba sai ya ci daga abun da ya halasta. 

Amma dangane da Idin layya an so wanda zai yi layya kar ya ci komai har sai bayan sallar idi sai ya ce daga dabbar layyan shi. 

Wanda kuma bai da dabban da zai yi layya babu laifi idan ya ci abinci kafin sallar idi. 

3️⃣ KABBARBARI A RANAR IDI 

Ibn Abi Shaibah ya riwaito da isnadi ingantacce daga Al-Zuhriy cewa: Mutane sun kasance suna yin kabbara a ranar idi daga lokacin da suka fito daga gidajensu har sai sun isa filin sallar idi sannan suna ci gaba da kabbarbari har sai liman ya fito... A duba Irwa'u al-Galil 2/121.

Sai dai lokacin kabbarbarin Idin karamar Sallah yana farawa ne lokacin da idi ya fara (ranar da aka ga wata) har sai liman ya fito sallar idi. 

Amma kabbarbarin sallar idin layya yana farawa ne daga daya ga watan dhul-Hijjah zuwa karshen ranakun ayyamut tashreeq. 

YAYA AKE KABBARBARIN? 

Ya zo a Musannaf na Ibn Abi Shaibah da sanadi ingantacce daga Abdullahi Ɗan Mas'ud, Radhiyallahu anhu: ya kasance yana kabbara a cikin ayyamut tashreeq: ALLAHU AKBAR, ALLAHU AKBAR, LAA ILAAHA ILLAAH, WALLAHU AKBAR, ALLAHU AKBAR WA LILLAAHIL HAMD. A wata ruwayar ya ce za a yi kabbara sau 3.

A wata har wayau daga Abdullahi Bn Mas'ud: ALLAHU AKBAR KABEERAN, ALLAHU AKBAR KABEERAN, ALLAHU AKBAR WA AJAL, ALLAHU AKBAR WA LILLAAHIL HAMD. A duba littafin Irwa'u al-Galil 3/126.

4️⃣ YI MA JUNA MURNA (BARKA)

Daga Jubair Bn Nufair, ya ce: Sahabban Manzon Allah, sallallahu alaihi wa sallama, sun kasance idan suka haɗu a ranar idi sashensu kan ce ma sashe: Allah ya karɓa daga gare mu da ku (TAQABBALALLAHU MINNAA WA MINKUM). Fathu al-Baariy 2/446.

5️⃣ YIN KWALLIYA DOMIN IDI

Jabir, Radhiyallahu anhu, ya ce: Manzon Allah, sallallahu alaihi wa sallama, yana da wata alkyabba ta musamman da yake sanyawa ranar Juma'a da ranar idi. 

Al-Baihaqiy, ya riwaito da isnadi ingantacce cewa Abdullahi Ɗan Umar, Radhiyallahu anhu, ya kasance yana sanya mafi kyawun kayan shi a ranar idi. 

Dangane da mata kuma haramun ne su sanya kaya mai kwalliya su fita da shi zuwa masallaci kamar yadda haramun ne su shafa turare. 

6️⃣ CANJA HANYA YAYIN DAWOWA DAGA IDI 

Hadisi ya inganta daga Jabir Ɗan Abdullahi, Radhiyallahu anhumaa, ya ce: Manzon Allah, sallallahu alaihi wa sallama, ya kasance idan ranar idi ta zo yana canja hanya. (wato idan ya je ta wata hanya idan zai dawo sai ya canja hanya). Bukhari ya riwaito 986.

Da fatan zamu nisanci duk wani aiki da zai bata mana ladan Ibadan da muka gabatar. 

Ni ma Ɗan uwanku Umar Shehu Zaria ina cewa daku: TAQABBALALLAHU MINNAA WA MINKUM. 

✍️ Ɗan uwanku a Musulunci:
Umar Shehu Zaria 

Comments

Popular posts from this blog

Addu'ar Neman Mijin/Matar Aure

TAMBAYA Assalamu Alaikum warahmatullah malam don Allah ina Neman fatawane Watace take Neman miji kasancewar duk masu  zuwa wurinta ba dagaske suke yi ba toh shi ne ta nemi taimako wurin malamin zaure yake bata rubutu tana sha daniyyar Allah ya sa ta dace. Toh malam abin tambaya anan shi ne shin menene makomar abin da ta aikata? shin malam tayi shirka ne ko kuwa tayi ba daidai ba? nagode. AMSA    Dafarko gameda shan rubutu muddin ayan QUR'ANI ne tsantsa babu wasu zane zanen hatimi, to ya halatta yadda IBN TAIMIYYA ya tabbatar a MAJMU'UL FATAWA, haka ma WAHEED ABDUSSALAM BAALY ya tabbar da hakan a SARIMUL BATTAR,    Amma in akasin haka ne haramun ne don yakan zama shirka ne da surkulle,    Fadin cewa Malamin zaure ne na gargajiya to galibi irin na shirkan sukeyi, don haka ki tuba tsakanin ki da ALLAH da alkawarin bazaki sake zuwa wurin su ba don kare addinin ki da mutuncin ki,    Don samun biyan bukatun ki sai kizage da addu'a da kiyamul...

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI Fitowa na 3

HAKKOKIN MA’AURATA A SHARI’AR MUSULUNCI               NA MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO, KANO. FITOWA TA 3 (kuma fitowa ta karshe): HAKKOKIN MACE A KAN MIJINTA: Kamar yadda miji yake da hakkoki akan matarsa, haka ita ma matar take da hakkokin akan mijinta, daga cikin wadannan hakkoki akwai : 1 - SADAKI: Hakkin mace ne a bata sadakinta, yayin da za a aure ta, Allah Madaukakin Sarki ya ce: “Ku bawa mata sadakinsu kyauta” (Nisa’i 4). A wani wurin Allah Madaukakin Sarki cewa ya yi:   “Ku aure su da izinin iyalansu, ku basu sadakinsu da adalci” (Addalak : 25). 2 – CIYARWA: Hakkin mata ne akan mijinta ya ciyar da ita, gwargwadon halinsa, koda kuwa tana da wadata da arziki, Allah Madaukakin Sarki yana cewa :  “Mai wadata ya ciyar daga wadatarsa, wanda kuwa aka kuntatawa arzikinsa, to ya ciyar daga abin da Allah ya bashi, Allah baya dorawa wata rai sai abin da ya bata” (Dalaq : 7). An tambayi Manzon Allah, tsira da amincin ...

HUKUNCIN HADA SITTU SHAWWAL DA RAMUWAR RAMADAN

Tambaya : Assalamu alaikum Malam idan ana binka ramuwar azimi za ka iya niyya biyu : wato da nufin sittu shawwal da ramuwar Ramadhana a guda daya ? don Allah mlm taimaka min da bayani. Amsa :  Wa alaikum assalamu To 'yar'uwa kowanne daban ake yinsa, saboda manufarsu ta banbanta, don haka ba za'a hada su da niyya daya ba, kamar yadda ake yi a wankan janaba da wankan juma'a, za mu fahimci haka, a cikin fadin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi : "Duk wanda ya azumci Ramadhana sannan ya biyar da kwanaki shida na Shawwal, Allah zai ba shi ladan wanda ya yi azumin shekara" Muslim ya rawaito shi a hadisi mai lamba ta : 1164, kin ga wannan yana nuna Ramadan daban, sittu-shawwal daban. Fadin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi : " Sannan ya biyar da kwanaki shida na Shawwal" ya sa wasu malaman sun tafi akan cewa : bai halatta ayi sittu-shawwal ba, sai bayan an kammala ramuwar Ramadan. Kamar yadda ya zo a : sharhurmumti...